Chapter 125

175 18 0
                                    

Ammabuwa dake kwance a uwar daka taji motsi kamar Ammi ta shigo, mikewa tayi daga kwancen da take jiki babu kwari ta lalaba ta fito. A kan kujera ta hango Ammi a kwance ko motsi batayi, wani irin harbawa kirjinta yayi tayo kanta a guje tana kiran "Ammi! Ammi!!"

Amma Ammi inaaaa, ganin Ammi ko motsi batayi yasa ta mike a guje ta nufi waje, ta soma kiran makwabta ta suzo su kawo mata doki, nan fa aka shishigo aka soma taimakawa a fita da Ammi sai asibiti.

Ammabuwa sai faman kuka takeyi, Suna isa asibiti straight aka wuce da Ammi emergency room, luckily Ashraf yana asibitin don dr Dangora yana tafiya aka dawo dashi yayi resuming aikinsa, hankalin Ashraf a tashe ya soma tambayar Ammabuwa meya faru, tana kuka tace itama bata sani ba, dawowan Ammi kenan ta fito ta taddata a hakan"Ashraf dan Allah Ku taimaka ku ceto mun Ammi kar na rasa ta please, ya Allah gani gareka wayo ni". Sai faman kuka take tamkar ranta zai fita.

Anty Rakata ranta a bace ta mike ta fita don ta kira Huda don tasan daga wajenta Ammi ta fito, gudun kar Ammabuwa taji yasa tayi nesa tukuna ta soma dialing number Huda, ringing buyi ta dauka zatayi mata magana cikin gatse kamar yanda ta saba, Anty Rakata ta dakatar da ita "wai ke wace irin mutum ce, yanzu fisabilillah me kika yiwa mahaifiyarki ta dawo haka?"

"Ban gane ba, meya faru?" Huda tambayeta.

"Toh Amminki dai an kawota asibiti rai a hannun Allah, sai kiyi sauri kizo"

"Innalillahi wa innalillahi raji'un, meya sameta?"

"Kinfi kowa sani". Anty Rakata ta bata ansa tana jan tsaki".

Hankalin Huda a tashe tace "wani asibitin?"

"national hospital"

"Toh gani nan zuwa".

Cikin sauri ta katse wayar, ta dauko gyalenta da makulin mota a kidime ta fito sai hanyar asibiti, a waya ta kira Muhseen ta sanar dashi halin da ake ciki, shima hankalinsa a tashe yace gashi nan zuwa.

Ammabuwa na zaune dasu maman Luba har yanzu kukan nata bai tsaya ba "Ammi fa lafiyanta kalau ta bar gida, bata fada mun inda zata ba, yanzu ya zanyi maman Luba, taya ma zamu fara biyan kudin asibiti? " ta tambaya, kuka takeyi sosai kamar ranta zai fita.

"Ammabuwa addu'a ya kamata ki dinga mata yanzu ba kuka ba, kuma batun kudin asibiti, ba Ashraf yace abar komai a hanunsa ba? Karki damu". cigaba sukayi da bata baki suna rarashinta.

Sai bayan 30 minutes tukuna Huda ta iso asibitin, tana ganinsu Ammabuwa ta karaso hankalinta a tashe ta soma tambayar Ammi, Ammabuwa ko kallonta batayi ba ta kawar da kanta gefe ta cigaba da kukanta, su Anty Rakata suka bata ansa sukace tana emergency har yanzu, bata tsaya wata wata ba ta haura sama, tana wani irin gudu kamar wata zarariya, cikin sa'a kuwa sai ga Ashraf ya fito a guje Huda ta karasa wajen shi tana fadin "Ashraf ina Ammi' na?! Dan Allah ka kaini inda take inaso ganinta! Inason na nemi gafararta i want to see her please!" .

Ashraf ya tsaya yayi shiru yana kallonta ya kasa cewa komai. fuskarsa babu walwala, kana ganinshi kasan yana cikin tsantsan tashin hankali, "Magana nake maka! Nace ka kaini wajen Ammi'na". ganin ya tsaya ya kasa bata ansa yasa ta juya  fusace zata nufa emergency room din Ashraf yazo ya sha gabanta yana fadin "i'm sorry Huda amma sai dai ki dau hakuri don Allah ya yiwa mahaifiyarki rasuwa".

Cak Huda ta tsaya, sanadiyar bugawa da kirjinta yayi daga bisani ta soma magana tana girgiza kai
"No karya ne! Ka daina mun irin wanan zancen bana so, Ammi'na bata mutu ba! Ka kaini inda take yanzun nan!".

"Kiyi hakuri Huda kafun mu shiga da ita cikin theatre ta cika, there was nothing we could do".

Matsawa da baya tayi ta jingina da jikin bango tana zaro ido don jin maganar Ashraf tayi tamkar a mafarki, cigaba da zaro ido tayi tana expecting yace mata ba gaskiya bane,  dataga yayi shiru sai faman binta da kallon tausayi yake yasa ta gasgata maganarsa ai kuwa bata san sanda ta fadi a wajen ta rushe da wani irin  kuka mai cin rai, kuka take irin wanda bata ta'ba yinsa ba cike da nadamar abunda ta aikata, Ashraf ya kasa ce da ita komai don bai ma san ta inda zai fara rarashinta ba,  a hankali ya juya jiki a sanyaye don yaje ya sanar dasu Ammabuwa, yana tunanin ma ta yanda zai fara.

You'll also like

          

Su Ammabuwa suna zaune, hankalinsu kwata kwata baya jiinsu, sai faman kwararo duka addu'ar data zo bakinsu sukeyi, Muhseen ne ya shigo hankalinsa a tashe,ya karaso yana tambayarsu Ammi, suka ce tana emergency har yanzu. Muhseen yace toh bari yaje yaji ko nawa ne zai biya kudin asibitin. Ammabuwa ta girgiza masa kai tace karya damu, Ashraf zaiyi handling, har ya bude baki zaiyi magana sai ga Ashraf nan ya karaso yana tafiya jiki a sanyaye, Ammabuwa na ganinsa ta mike cikin sauri ta karasa inda yake ta soma tambayarsa "ya Ashraf, ya  jikin mamata?  ta farfado?!"

Shiru Ashraf yayi yana dubanta da idanunsa da suka kada sukayi jazir tsabar tashin hankali " kiyi hakuri Ammabuwa, mun kasa yiwa mahaifiyarki komai don kafun mu shiga da ita ta cika, yanzu addu'ar mu kadai take bukata don....".

Ai bata bari ya karasa maganar ba sake wata irin razananiyar kara ta fadi a wajen sumamiya, nan da nan aka rufu akanta aka shiga bata taimakon gagawa, su Anty Rakata suma kuka, Muhseen hankalinsa a tashe a tashe ya soma neman matarsa, ya haura sama, nan ya hangota ta jingina da jikin bango, tana wani irin kuka, a kidime ya karasa ya kamota tana ganinshi kukan nata ya karu ta fa'da jikinsa tana wani irin kuka mai cin rai.

Da kyar dai aka samu Ammabuwa ta farfado, tana bude idaunta wani sabon kuka ya fara, kuka takeyi irin wanda bata taba yinsa a rayuwarta ba har kusan karamar hauka tayi, su Anty Rakata ne kadai suke ririke da ita, cikin daren dai sunga tashin hankali don sumanta kusan uku. Muhseen tunda suka isa gida ya kasa gane kan Huda sai faman kuka takeyi tana fadin "ya zanyi da rayuwarta yanzu? ban nemi gafararki ba Ammi, ban samu na nemi gafararki kin yafe mun ba, kin mutu da bakin cikina da kuma tsanata a ranki".

"Amminki bata tsaneki ba Huda, na ta'bbata da ta yafe miki tunda har ta tashi ta biyoki Abuja, mahaifiyarki na sonki Huda don har ammanrki ta bar mun a hannuna kafun ta tafi".

Kawar da kanta gefe kawai tayi ta cigaba da kukan don ita kadai tasan me take yiwa kuka. Muhseen babu irin rarashin da baiyi cikin daren nan ba amma ta kasa daina kukan.

A cikin daren mafarke mafarke ta dinga yi, ta dinga ganin kanta cikin wani filli ita kadai tana faman ihun sunan Ammi "Ammi' na kina ina?! Ammi...!"

Muryar Ammi ta ji yana tashi inda take fa'din "ki tafi ki bani wuri bana bukatan kudinki Huda, nace bana bukatansu". Kudine suka soma zubowa daga sama, Huda ta durkushe a wajen tana ihu tana kiran sunan Ammi.

A firgice ta farka daga baccin da take , zufa na karyo mata ta ko ina, Muhseen dake kwance a gefenta shima a kidime ya farka ya rukota yana tambayarta lfy? "Muhseen Ammi ce... na ganta a mafarki, tace mun bata sona na tafi na bata wuri".
Ta karasa maganar tana kuka.

Rarashinta Muhseen ya shiga yi, karshensa ma rufeshi da fada da masifa tayi tace ya rabu da ita, laifinta ne Ammi ta rasu? meyasa zata dinga irin wanan mafarkin, maganganu dai ta dinga yi cikin daren tamkar mai ta'buwan hankali.

Washe gari da safe, gidansu Ammabuwa ya cika da mutane, yan unguwa kuwa kowa sai daya girgiza da jin mutuwar Ammi don mace ce mai son mutane, ta zauna da kowa lafiya, an cika a gidan kuwa, Ammabuwa tana kule cikin daki, daga ita sai Anty Rakata da maman luba suna faman aikin rarashinta, gabadaya tayi wani iri ta gama fita hayacinta, fuskarta ta kode saboda kuka, wani irin zafi takeji cikin zuciyarta ke mata taya zata fara rayuwa yanzu babu Ammi? bayan an gama suturta Ammi, aka kirata dakin da Ammi take kwance don ta mata addu'a, kuma ta nemi gafararta. Ammi na kwance fusakarta sharr kamar an dauke mata duk wata nauyi a rayuwa, inka ganta tamkar mai bacci, Ammabuwa ta karasa ta tsuguna gabanta tana wani irin kuka, sai datayi mai issanta tukuna ta soma fadin "Ammi kin tafi kin barni, ya Ammabuwa zata yi rayuwa babu ke? Ammi kin daukar mun akawirika da dama ciki harda burin kiga ranar aurena, da kuma ya'yan da zan haifa kiga jikokinki amma sai yau gashi na wayi gari babu ke Ammi'na, Ammi naso ace nice zan share miki hawayenki don ki wahala damu, Allah yasa karshen wahalar kenan, Allah ya kai haske kabarinki, yasa kin huta, Allah ya sadaki da gidan aljana, kuma ya karbi bakoncinki cikin rahamarsa". Sosai Ammabuwa ta cigaba da yiwa Amminta addu'a tana kuka, sai da aka shigo aka dagata a wurin tukuna ta mike ta fito tana kuka.

Kowa sai sannu yake mata ta share hawayenta zata koma daki, harta sa hannu zata da'ga labule taji wata magana dayasa ta dakatawa, muryar Anty Rakata ta soma ji yana tashi daga dakin inda take fa'din "ai daga wajen Huda ta fito ciwonta ya tashi, tun daga lokacin ba sake samun kanta ba".

Cikin sauri Ammabuwa ta daga labulen ta karasa dakin hankalinta a mugun tashe, Anty Rakata na ganinta ta soma zaro ido don basu san tana wajen ba.

Ana cikin haka sai ga Hudan ta shigo cikin gidan tana ihun kukan mutuwar Ammi, kamar wace ta zare, kowa kuka yakeyi irin wanda musulunci ya yarda dashi amma ba irin na Huda ba, tana ihu duk tabi ta tadda hankalin kowa, Ammabuwa najin kukanta ta mi'ke a fusace zatayi waje su Anty Rakata suka ririketa "ina zaki kuma Ammabuwa?"

"Zanje na sami muguwan nan azaluuma wace ta kashe mun mahaifiya, dole ta bar gidan nan yau". Ammabuwa ta karasa maganar ta fuzge tayi cikin gida, tana ganin Huda tayi wani irin kukan kura zatayi kanta mutanen wurin akayi caa aka ririketa "ki fita ki bar gidan nan nace! Banso na kara ganinki, hankalinki ya kwanta kin kashe mun muhaifiya! Ita kadai ce ta rage mun a duniya yanzu kin rabani da ita, kin sani sarai batada kosaahen lfiya amma sai da kikaga bayanta, kece mutum ta karshe data gani kafun ta rasu, duk ke kika jawo! Bazan ta'ba yafe miki ba Huda! Ki fita nace". Sai faman fuzge fuzge Ammabuwa take tana wani irin gunjin kuka ana rike da ita.

Daya daga cikin matan wurin tace "Haba Ammabuwa ya kike irin wanan maganar ne, itama fa yar'uwarki ce. Ya za'ayi kice itace ta kace mahaifiyarku, ki yarda lokacin Amminku ne yayi, kuma yanzu haka ba wanan abun take bukata daga gareku ba, addu'arkuce kadai take bukata.

"Wlh nayi rantsuwa babu kaffara itace ta kashe mun mahaifiya! Ta fita nace bana son ganinta! Kuce mata ta fita!"

Hawaye na zubawa Huda tace "ki daina fad'in haka ya' Ammabuwa wlh bani na kashe Ammi ba, Ammi nima mahaifiyata ce, yanda kikeji haka nakeji, wlh bani na kasheta ba". Sai faman kuka take wiwi hawaye na zuba mata, wasu mata ne suka taho suka sa hannu aka shige da Ammabuwa ciki. Ita kuma Huda aka ce ta shiga ciki don ta yiwa mahaifiyarta addu'a ta nemi gafara, tana isa ciki ta tsuguna gaban gawan Ammi tana wani irin kuka,Gabadaya illahirin jikinta har wani irin girgiza yakeyi tana kuka ta soma fa'din "Ammi.....duk duniyar nan babu wanda ya kaini kaunar ki, inasonki Amm'i na, kece kika kasa fahimta ta, ke kadai a duniyar nan kike kaunata,, yanzu gashi na rasa ki a sanadiyar rashin tauna maganata kafun na furta, ban baki darajarki ba Ammi a matsayinki na mahaifiyata, ki yafe mun Ammi'na, nayi kuskure kuma na tuba dan Allah ki dawo gareni, wayyo ni Allah , dan Allah Ammi ki dawo karki tafi ki barni, na canza halayena!". Sai faman kuka takeyi tamkar ranta zai fita, da kyar aka samu akazo aka bambarera daga jikin Ammi.

Huda na fitowa tsakar gidan, aka jiyo ana kallonta, wasu na magana kasa kasa, wasu kuma  har da hararta suna aika mata mugun kallo na cewa itace ta kashe mahaifiyarta, don tabbas sun san zata iya aikatawa don babu wanda baisan yanda Ammi take fama akanta ba, dataga abun ya soma yawa, ta kasa juriyar kallon banzan da mutanen wajen suke mata, ta mike ta bar wajen cikin sauri tana hawaye ta kira Muhseen daya zo ya dauketa.

Bafi 10minutes ba sai gashi nan ya taho,
Huda na ganin Muhseen ta fashe da wani sabon kuka,ta fada jikinsa tana fa'din "Muhseen meyasa mutane suka tsaneni ne haka? Meyasa sukaki jinina? Meyasa bazasu barni na numfasa ba? A gaban mutane ya' Ammabuwa take fadin wai ni na kashe Ammi, Ka yarda nice na kashe Ammi?".

"No no sweetheart please ki daina fadin haka, yayarki tana fama da zafin mutuwa ne shiyasa take fa'din haka amma karki bari maganganunta suyi tasiri akanki, bake kika kashe ta ba, kiyi hakuri please mu koma ciki".

Ta girgiza masa kanta tace "bazan iya komawa ba dan Allah ka daukeni anan, I can't stand it".Ruko hannunta yayi yajata cikin motar suka bar unguwan.

Ba tare da ba'ta lokaci ba aka gama shirya Ammi aka mata sallah sa'anan aka kaita gidanta na gaskiya.


Allah ya jikanki Ammi🥺

HUDA🔥 BOOK 2Where stories live. Discover now