*GASHIN ƘUMA*
Na
© Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabirPage 2.
Bilal ya nufi bangaren masu aiki, ta can baya aka ware na masu aikin gidan, daki ciki ɗai ɗai ne a jere guda uku sai bayi a gefe mai hade bayan gida da wanka, yana isa sashin ya kwada sallama ba tare da ya buga kofa ko daya ba, dan bai san wanne ne dakin Musa mai wanki ba, saboda akwai dakin mai gyaran fulawa da sharan gidan da kuma na mai wanki sai kuma na drivern momy, ko wanne da dakinsa ba takura, Musa ne ya fito daga bayi alamun yayi alwala cikin sakin fuska yace.
Karamin Alhaji kai ne da kanka kazo nan bangaren, ai da ka aiko mun zo gareka dan cika bukatarka.
Karka damu, na zo wajenka ne ka ara mini kaya dan na san kana da tsafta, ka duba mini wanda suka ɗan koɗe, ka bani inna gama amfani dasu zan dawo maka damu.
Karamin Alhaji me zakayi da kayana? ai kafi karfinsu sai dai...
Bana son jayayya ka shiga ka fito mini da jakar kayanka na zaba.
Cewar bilal daya katseshi, da sauri Musa ya shiga dakinsa ya dauko gana mazgo dinsa ya dire a gaban Bilal.
Ai ko duka kace sunyi maka to ka tafi da su yallabai.
Bilal bai ce komai ba ya tsuguna ya bude jakar ya shiga duba kayan, abinda ya burgeshi har ya kwantar masa da hankali yadda yaji kayan suna kamshin turare duk da ya gane irin turaren nan ne mai arha, amma yaji natsuwar saka kayan dan Musa akwai tsafta, ya dibo riga shirt da wando jins wanda suka dan sha jiki amma fes suke, sai ya dauki wata shadda riga da wando wanda dinkinsa yake tazarce, duk da tadan yi haske amma yana da kyan gani, yana gama dibansu ya mike yayi gaba ba tare da yace komai ba, Musa ya bishi da kallo yana girgiza kai cike da mamakin wannan lamari, yasan dai da akwai abinda Bilal zai yi mai muhimmanci da yasa shi daukar kayansa, ajiyar zuciya ya sauke yana cewa.
Allah ya sa Alkhairi ne.
Sai ya dauki jakarsa ya mayar daki ya fito ya nufi masallaci. Bilal kuwa yana isa daki ya saka kananun kayan ya adana shaddar kana ya fesa turare a jikinsa sai ya dauko wani p-cap ya saka a akansa ya dauko key da wayarsa ya fito, alla alla yake kar wani ya ganshi, har ya fito falon bai yi karo da kowa ba sai da ya isa parking space ne yana kokarin shiga mota sai ga Yaya Abdul ya fito daga motarsa da shigowarsa kenan yayi parking, yana ganin Bilal yadda yayi wani shiga kamar bai da gaskiya ya sashi yin sauri ya isa wajensa yana dubansa, shima Bilal kallonsa yake fuska daure dan sam bai so ya ganshi ba, Abdul yace.
Yau kuma shaye shayen da kayi irin shigar daya saka kayi kenan? Ko kuma club dinku suka saka gasar saka kodaddun kaya saboda hauka. Ina fatan abinda ya sameka karya samu sauran dangi, Allah ya shiryeka.
Ameen, malam ban son sa ido babu ruwanka da rayuwata ehe, munafuki kawai na tabbatar kan na dawo ka fesawa su Momy dan halinka kenan gulma.
Cewar Bilal a hasale kana ya bude mota ya shiga tare da rufe motar da karfi kamar da shi yake fada, Abdul murmushi kawai yayi dan ya saba da halin Bilal duk da ya girme masa amma sam baya ganin girmansa saboda basa shiri, basa zama a inuwa guda dan halinsu ya bambanta, Abdul mutum ne mai hankali da natsuwa ga ilimi da sanin yakamata kuma shi mutum ne da bai da magana, sabanin Bilal da shi sam baida hakuri ga surutu da raina mutane, hasalima shaye shayensa yasa baya ganin kowa da gashi Abba da Momy ne kawai yake dagawa kafa, shi kuma Abdul baya taba ganin kuskuren Bilal yayi shuru dole sai ya tanka, shi kuma bilal sai ya rama tare da yi masa rashin kunya, haka suke zama tamkar annabi da kafiri sai kace ba jini daya suke ba.
Albdul yana shiga ya samu momy a falo ya gaisheta ta amsa masa tare da tambayarsa aiki, ya zauna yana share gumi yana cewa.
Aiki Alhamdulillah yau ma banyi wani aikin kirki ba saboda jikina ba dadi sai kuma yawan gumi da nake yi ga faduwar gaba.
Subhanallahi wai har yanzu baka daina jin wannan yanayin ba, Abdul kaje a yi maka check up gaba dayanka dan Allah, dan kar wani ciwon yazo ya shigeka.
Momy nayi fa gwajin sugar ba shi bane, sannan kusan kullun saina gwada bp na, ulcer ce kawai ke damuna kuma ina kan shan magani.
Allah ya kara sauki sai ka cigaba da kula da cin abincinka, duk da nasan kai baka wasa da cikinka.
Ni ai ulcer ta ciwo ne daga Allah dan bana wasa da abinci. Ummm kin ga mutuminki Bilal kuwa yanzu da zai fita?
A'a ai ban san ma ya dawo ba.
Abdul ya yi guntuwar dariya kana ya shiga bata labarin irin shigar daya gani a jikinsa, momy murmshi ta yi tana yi masa fatan shiriya dan ta san lamarin bilal ya yi nisa sai addu'a.
*****
Bilal.
sai da ya kusa isa kwanar kwadayi kafin ya samu waje yayi parking motarsa a gefen hanya kana ya fito ya rufe da key ya taka a kafa har ya isa wajen, duk da gari ya soma duhu saboda har an fito sallar magrib, ya gane Humaira saboda akwai hasken wutar lantarki dake ta bayanta na shagon me sai da tsire, sannan akwai karamar tocila a hannunta da take haske kaskon suya, a hankali ya isa gabanta ya tsaya ya rusuna tare da mika naira dari biyu yana cewa.
A bani awara na dari kar a saka yaji.
Humaira ta dago ta amsa kudin ta shiga saka masa a farar ledan santana, tana gamawa ta mika masa tare da chanjinsa, ya amsa sai ya isa wajen me tsire ya samu benci ya zauna yana kallon bayanta, ganinta da yayi tabbas ya tabbatar da ya kamu da sonta dan wani fusgarsa zuciyarsa keyi yana kara kawata masa kyanta sosai duk da fuskar fayau take ko kwalli bata saka ba, sannan karin farin cikinsa karamar yarinya ce daidai irin yadda yake so dan yaji dadin juyata son ransa.
.....
Humaira.
Hafsat ce ta zo ta karbeni da suyar tana bani labarin baba ya dawo da ragon layya daya sayo a kauyen makarfi, nayi farin ciki da fatan alkhairi sai a lokacin na tuna da dinkina wanda ban amso ba saboda ba a dinka mini da karamar sallah ba dan nakai latti, nace cikin doki.
Allah yasa Fatsima tela ta gama mini dinkina dan ina so na saka a ranar idi.
Haba ai ko ya isa ta gama tunda an biyata kudin dinkin. Gobe In Allah ya kaimu sai muje mu karbo.
Cewar hafsa, sai nace Allah ya kaimu, ta amsa da amin. Kala biyu na samu na kayan sallar, kaka ce ta siya mini daya shine ban samu dinkinsa ba sai kuma wanda Umma ta dinka mana ni da hafsat atamfa ce aka dinka mana doguwar riga, shine muka saka da karamar sallah, duk cikin gidanmu nice na samu kala biyu amma sauran daga me kala hudu sai biyar, ko hafsat hudu gareta dan baba yayi mata kala biyu kanwar umma ta kawo mata daya, Indo kuwa kusan shida gareta saboda duk cinikin da nayi na awara kafin azumi akanta Inna Hajjo ta karar da kudin, a cewar ta itace budurwa dan ta girme mini da kusan shekara uku, sannan dansu take niman kudinta, koda kaka tayi mata korafin meyasa bata dinka mini ko atamfar roba bace, tace ba zata yi asara ba tunda ba son sa kaya nake ba kuma ko wanka bai dameni ba balle nayi kwalliya dan haka ba zata siya ba, kila nan gaba in na san darajar kaina ta siya mini, murmushin yake kawai nayi ban nuna damuwata ba saboda duk zancen a gabana suka yi, amma cikin zuciyata abin ya bata mini rai sai dai bani da halin nunawa, nike shan wahalar amma masu cin gajiyar suna gefe, sannan saboda sharri wai nice bana wanka, wanda duk gidan nan inna cire Umma babu wanda ya kai tsafta ta dan har kwatance umma take yi dani in tana yiwa Hafsa fadan ta rika yin tsafta.