*LOKACI NE...!*
_Fitattu Biyar_©️ *OUM MUMTAZ.*
_No: 8_
_Free Page_"Kiyi haƙuri Umaima, ki yafe min dan Allah! Wallahi ban ƙara auren nan da niyar cin amana ko kuma tozarta ki ba." Lawal ya faɗa ma Umaima da take kwance kan doguwar kujera mai cin mutum uku,tin bayan tafiyar Innayo.
"Na riga da na faɗa maka, babu komai na yafe maka dik da nasan ni baka min laifin komai ba, amman ina neman alfarmar ka barni na fara sana'a, sannan naci gaba da karatu na, tinda kaga daman dalilin auren mu nayi diapering." Umaima ta faɗa muryarta a sanyaye, wanda har cikin zuciyarta bata jin kishin Lawal ɗin da hakan yake bata mamaki, a ranta tana addu'ar Allah ya daura ta akansa.
Lawal da daman naiman abinda zai faranta ma Umaima rai yake babu gardama yace,"Na amince lamince miki Umaima, ki kama sana'a, sannan kuma kici gaba da karatunki, amman kuma kinsan sha'ananin kasuwa ta bazan iya daukar nauyin karatunki ba saboda yanda abubuwa suka taɓarɓare mana a wannan marrar da muke ciki?" Ya ƙare maganar yana ɗan ɗinke fuska haɗi sosa kai, wanda hakan yasa Umaima murmusawa ba tare da ta shirya ba, a ranta kuwa faɗi take mai hali dai bazai taɓa chanza halinsa ba.
"Kar ka damu da batun ɗaukar nauyi na, tinda kaga daman shekara ɗaya ce kawai ya rage na kammala, kuma daman kaga yanzu zanyi registration na first semester level 4 cikin satinnan da naji ance an fara,kasan sai da na rubuta exam na second semester level 3,kuma results da ya fito Alhamdulillah bani da matsalar carry over ko guda ɗaya." Umaima tayi maganar tana kallon Lawal da har ya saki fuska jin cewa zata ɗauki nauyin karatunta ba tare da yabi ba'asin inda ta samo kuɗin ba, wanda ita daman tasan cewa tin farko zallar maƙo da ƙin fidda kuɗi irin na shi ne ya hana shi ya barta taci gaba da karatun ta, amman sai ya fake da cewa wai shi bashi da ra'ayin matarsa tayi karatun boko, wanda ita kuma a lokacin da yake giyar soyayya na ɗibanta, babu gargada ta amince da abinda ya faɗa, sai daga baya ta fuskanci alkiblar sa na tsantsar son kuɗi da ƙin kashe su.
"Ah to masha Allahu abu yayi kyau, Allah yasa ki fara a sa'a. Mai kike son ci naje na kawo miki? Naga alama ko karyawa baki yi ba har yanzu tinda na shigo Amir sai faman kuka yake amma baki jisa ba"
"Kai da ka bar amarya a gida, ai bai kamata ace kazo ka tare anan ba Abban Amir, kawai ka tashi ka tafi,ni kuma kar ka damu zan tashi na nemawa kaina abinda zanci." Inji Umaima da ta tashi daga kwancen da take, fuskar ta da murmushin karfin hali, wanda tin dazu shi take sabida ya boye mata yanayi na ƙunci da take fama da shi.
"Kar ki damu da amarya, dan Allah ki faɗi abinda za ki ci naje na kawo miki na hutar dake." Lawal ya faɗa ba tare da ya maida hankalinsa akan zancen amaryarsa da ta masa ba, wanda dik wani abinda ake ta faman yi tin dazun tana nan maƙale cikin zuciyarsa sabida ba rabuwan dadi suka yi ba kafin ya fito, akan yace zai tafi wajen Umaima, ita kuma ta dage sai ta bisa yace ba zata ba.
"Ka karbo min awara to." Inji Umaima a taƙaice ganin Lawal ya dage sai ya kawo mata, sabida so take yayi ya tafi ya bata wuri ta zauna tasha kukanta da take kokarin dannewa, wanda daman ita kuka ya jima da zama abokinta ba wahala yake bata ba.
Da rawar jiki kuwa Lawal da yake jin shakkar Umaima ya fice, a ransa kuwa kima da kuma kaunarta kara yawa yayi a cikin zuciyarsa sabida bai taba tsammanin magana ta arziki zai sake shiga tsakanin sa da ita ba idan taji labarin aurensa, amman sai gashi ta basa mamaki kwarai da gaske wanda wani ɓari na zuciyarsa yake tambayar sa anya kuwa ma tana son sa kaman baya?.
Wanka ta shiga, bayan ta miƙa Amir tsakar gida wajen yara, da yake yau babu makaranta. A dai-dai sanda ta fito daga wankan Lawal ya shigo daga sayo mata awarar, wanda ya ɗan jima sakamakon layin da ya tarar a wajen, tare suka shiga parlon, Umaima ta shige daki, shafa mai tayi, sannan ta zabo wani less ɗinta da ta ɗinka a auren Aunty Hamida, sosai ɗinkin riga da skirt ɗin yayi mata kyau, ya kuma dace da farar fatar ta mai daukan idanuwa. Powder ta shafa, sai kuma lips glow mai danko da ta shafa a labbanta masu dan kauri da suka kasance kalar pink mai duhu. Sosai tayi wani irin kyau na ban mamaki bayan ta daura ɗankwalinta na network, kasancewar ta kyakkyawa son kowa ƙin wanda ya rasa, wacce take da diri mai ɗaukar hankalin dik wani lafiyayyen namiji(coca cola), wai don ma a hakan yanayin ta ya sauya sakamakon fitina da tashin hankalin da Lawal yayi ta faman wulla ta a cikin tsawon zamansu, ga kuma matsalolin yan gidansu da ya sako ta gaba.
Sosai ta mugun tafiya da hankalin Lawal a sanda ta fito, bugu da kari ga kuma wani kamshi mai sanyi na musamman da yake tashi a jikinta. Umaima zama tayi a kan kujera, taci awarar ta a natse kaman babu wani abinda ke damunta cikin zuciya.
"Zan je can unguwar, idan na dawo akwai magana mai mahimmanci da za mu yi da ke." Lawal yace a lokacin da yake mikewa tsaye hadi da gyara karin hularsa ta zanna da ke kansa.
"To a dawo lafiya, ina son zuwa gida, daga can kuma zan tafi bakin kasuwa akwai kananun abubuwan da nake son saya dan Allah."
Kallon ta yayi kaman banzai amince da tafiyarta gidan ba, sabida yana tsoron kar ta tafi gidan a cikin wayannan yayun nata da yaga suna masa kallon tara saura kwata, a samu wacce za ta zuga ta, tazo tayi masa bore, amman kuma da ya tuna cewa akwai mahaifiyarta da Umaiman take bukatar lallashin mahaifiya a wannan gaɓar babu tantama idan yace kar ta tafi gidansu bai mata adalci ba, hakan yasa shi faɗin, "To sai kin dawo, ki gaisar min da su Ammahn, anjima da yamma nima zan shiga mu gaisa da su, ga wannan dari biyar din kiyi kudin mashin, wannan dubu biyun kuma ki samu ki sayi wasu abubuwan da baza a rasa ba." Ya mika mata dubu biyu da dari biyar, tasa hannu biyu ta karba tare da godiya, a ranta kuwa fadi take, 'dik da ina da kudi, amman raba arne da makami ma ibada ne.'
****
"Umma ina wuni." Umaima da shigowarta gidan nasu ta faɗa cike da girmama wa, a lokacin da take ma kanta mazauni kan carpet dake cikin parlon Umma.
"Lafiya lau, yau kuma fitowar mai kika yi?" Umma ta tambayi Umaima tana wani ɗaure fuska kamar wacce taga maƙiyarta.
"Babu komai Umma, daman zuwa nayi na gaishe ku, sannan na faɗa muku auren Abban Amir da akayi sanda nake nan gida." Umaima ta faɗa tana danne zuciyarta na ganin irin kallon ƙasƙancin da Umma take mata, wanda ba don albarkacin Maimuna, da kuma nasihar mahaifinta da take tunowa ba, babu abinda zai sa take girmama ta, sabida muguwar kiyayyar da take nuna mata tin ba ta kai haka ba.
"Da kuma yayi auren nasa shine me? Ni a matsayi na na waye ɗinkin za kizo ki faɗamin? Allah ya kara, yasa yanzu ma idan kika koma ki tarda ya ƙaro wasu matan guda biyu ku zamo ku huɗu kenan, kinga kenan anan ne zan san cewa an miki kishiyar sai kiji dadin zuwa kina fada min, tashi ki bani wuri malama!"Umma ta ƙare maganar tana nuna mata hanyar ƙofa, da yasa Umaima miƙewa ta fice ba tare da ta kara second guda ba. Tsaki Umma ta buga taci gaba da jan charbin hannun ta, wanda ita wallahi bata san miyasa taji ta masifar tsanar yarinyar nan ba tin tana kankanuwarta, wanda take yawan hantarar ta a bayan idon Ammah, sai kuma ta samu lasisin musguna mata ɗin mai kyau ko a gaban Ammahn ne sabida ganin yanda itama take musguna mata kaman ba itace ta haife ta ba, ta laɓe a bayan bijire ma umarnin su na auren talaka da Umaima ta zaba sama da mai kuɗi.*Umaima*
Ɗakin Ammah ta shiga bakin ta dauke da sallama bayan fitowarta daga dakin Umma, wanda ta zabi shiga nata ɗakin kafin na mahaifiyarta sabida kara irin nata, amman kuma sai gashi ta tarda rashin mutunci da zallar baƙin ciki.
"Ina wuni Ammah." fadar Umaima.
"Lafiya, yaya kike?" Inji Ammah tana kallon Umaima da kanta ke kasa.
"Lafiya lau, ina Amina?" Ta tambaya tana wasa da yatsun hannun ta, Amir kuma yana dan ta'adinsa, wajen wasu kwanuka bayan ta ajiyesa.
"Babu jimawa ta tafi gidan Hamida, mijinta ya kira ba taji dadi ba tin jiya da ta koma." Ammah ta fada tana matsa kafafunta.
"Allah ya bata lafiya, zan shiga na duba ta idan na tashi daga nan." Umaima ta ce a sanda take matsowa kusa da Ammah, ta ɗauki kafar Ammahn ta ɗaura akan cinyar ta tana matsa mata kaman yanda taga tana yi.
Shiru dik suka yi na tsawon sakanni ba tare da sun sake cewa komai ba, Ammah tana kula da cewa akwai magana a bakin Umaima, wanda hakan yasa ta ɗan taɓe baki, a ranta kuwa fadi take 'kadan ma kika gani idan dai kika ce kin zabi zama da matsiyaci sama da mai kudin da na kawo miki ki aura,wanda nake ganin zan iya fanshe ko da rabin dawainiyar wahalar da nayi ma rayuwarki ne, amman sabida bakin ciki da hassada da ki ka gado, ki ka saka kafa kika ture', a zahiri kuwa cewa tayi, "Lafiya kuwa? Naga kaman da magana a bakinki?"
Umaima kuwa da daman ta rasa ta inda zata faɗi ma Ammah abinda ya kawo ta sabida ba taga fuskan hakan ba, ba tayi nauyin baki ba jin Ammah ta tambaye ta da kanta tace, "Ammah daman zuwa nayi na fada miki Abban Amir yayi aure." Tayi maganar kanta a sunkuye idanunta na cikowa da hawaye, zuciyarta cike da rauni da take ta ƙoƙarin dannewa.
Da mamaki sosai Ammah tace, "Aure kuma haka nan kaman wasan yara shine baki faɗa mana ba sai yau?"
"Nima bai fadamin zai yi aure ba, kawai yau da safe da ya zo gidan tare da yayar Babansa take fadamin an daura masa aure washe garin sadakan uku na rasuwar Baba." Umaima ta ƙare maganar tana mai fashewa da wani irin kukan da ya taso mata tin daga ƙasan zuciyarta, wanda bata samu daman yi ba a ɗazun.
Shiru Ammah tayi tana jujjuya lamarin cikin zuciyarta kaman ba za tace komai ba, sai kuma ta saki wani malalacin murmushi ba tare da ta bari Umaima ta ganta ba, "To ke kuma da ta faɗa miki mai kika ce a lokacin?" Ta tambayi Umaima da take ta faman kuka har zuwa lokacin.
Kukan da take bai bata damar amsa ma Ammah tambayar da tayi mata ba,wanda hakan yasa Ammah taɓe baki a fakaice taci gaba da karanta hisnul Muslim da take karantawa a lokacin da Umaima ta shigo ta ajiye.
Shiru Umaima tayi daga kukan da take sakamakon sallamar wasu mata da taji, wanda take kyautata zaton masu zuwa ma su Ammah ta'aziya ne.
Takai awa daya da rabi, wanda tayi tunanin Ammah za tayi mata nasiha da kuma yan shawarwarin da zai taimaka mata wajen ganin ta zauna da mijinta lafiya tare da abokiyar zamanta, amman kuma sai taga ko ta kanta babu wanda ya sake bi a gidan idan aka dauke Sulaiman ɗan Ammah da yake bin bayan Yaya Abubakar wanda ya shigo gida cin abincin rana.
Hakan yasa jikanta bala'in yin sanyi, ta ɗauki Amir ta goye sa, ta kuma saka hijab da niƙaf ɗin da ya taimaka mata wajen boye yanayin da fuskarta ke ciki tayi musu sallama.
Kamar yanda tayi alkawari kuwa kasuwa ta wuce da kudin da taje ta ciro jiya, wanda abinda ta kashe baifi dubu biyu ba da yake a lokacin rayuwa ba tayi tsada ba. Abubuwan ta na amfani irinsu moɗa, faka, soson ƙarfe, ashana, bucket, tsintsiyar laushi da na kwakwa da dai abubuwan da baza a rasa ba ta saya ta zuba su a wani babban bako da ta saya, sannan ta bada ajiyarsa a wajen wani dattijo, sai kuma ta shiga cikin kasuwa wajen masu sai da yadin hijabai, kaloli mabambanta masu ɗan yawa ta yanko, da kuma yadikan da ake dinka huluna na yayi da dik wani abin da tasan za ta bukata kafin ta fito tazo inda ta bada ajiyar kayan ta, ta karɓa tayi godiya ta hau machine tayi gida.
A matikar gajiye ta shigo gidan, wanda hakan yasa ba ta wani tsaya wajen su Hauwa'u da suke zaman kashe wando ba tsakar gidan kaman yanda itama ake yi da ita a baya. Sai da taci guntun abincin da ta rage dazu sabida yunwar da yaci kaniyar ta tinda a gidan na su ko albarkacin hakan ba ta samu ba, sannan ta yi sallar azahar da la'asar ɗin da ba ta samu damar yi ba. Tuwon shinkafa da miyar ɗanyen kuɓewa tayi dai - dai cikin ta da zai ishe ta har da ɗumame tayi, wanda kafin ta gama magriba ya kawo kai, sannan tayi wanka, ta karɓo Amir da yau Allah ya taimake ta Ƴar rigimar da ya saba yi mata bai yi ba.
Misalin ƙarfe takwas na dare Lawal ya shigo, tayi masa sannu da zuwa, ya amsa da sakin fuska a ransa yana gode ma Allah da ya azurta shi da mata kamar Umaima.
Da yake Amir har yayi bacci, Lawal ya kama hannun Umaima suka shige cikin dakinsu na ciki, bakin gado ya zaunar da ita, sannan ya wuce zuwa bangaren da kayansa yake ya janyo wani file daga can ƙasan kayansa Umaima na kallon sa. A gefen ta ya zauna shima sannan ya ajiye mata file ɗin akan cinyar ta, ita kuma ta bisa da kallo ne neman ƙarin bayani ba tare da ta buɗe baki tayi magana ba. Fahimtar hakan da Lawal yayi ne yasa shi faɗin, "Maganar da dazu nace miki zan zo muyi daman ba akan komai bane sai akan wannan file ɗin da yake ajiye kan cinyarki, takardu ne na can gidana da na gida inda na ajiye Lawisa,wanda da farko niya ta daman za mu ƙaura ne daga wannan gidan, sai kuma gashi abinda Allah ya ƙadarta bai yi kan cewa kece za ki fara rayuwa cikin wannan gidan ba, in dai takaice miki bayani wannan takartar mallakar gidan ne da dama da sunan ɗana Amir na gina sa, kuma mallakinsa ne halak malak ko da ace bayan rai na ne ban yarda gidan a saka shi cikin gado na ba sabida ba nawa bane na Amir ne, don haka gashi nan ki ajiye sa a wuri mai kyau kiyi masa kyakkyawar kulawa ina fatan kin fahimta? "
A hankali Umaima tace,"Insha Allah." A ranta kuwa mamaki ne fal, ashe dai Lawal har gidan kansa ya gina kuma ya saka amaryar sa a ciki bayan ga ta nan ita kuma ya ajiye ta a cikin gidansu da babu komai cikinsa sai zallar gulma da munafurci da son ganin mutum ya naima a ƙarkashinsu? Amman babu komai tinda gashi nan za ta kama sana'a, sannan jibi monday za ta je tayi registration wanda za'a fara attending na lectures sati uku masu zuwa, wanda za tayi amfani da wannan dama ta sati ukun wajen zaman ɗinka huluna da hijaban da za take kaiwa ƴan matan jami'ar da ta tabbata ba ƙaramin ciniki za tayi ba duba da cewa har zuwa lokacin ba a fara yayin hijabai da huluna na zamani ba a cikin garinsu, wanda itama ta koya ne a lokacin da ta raka Maimuna hutu can gidan ƙanwar Umma acan babban birnin ƙasar tasu. Kuma Allah cikin ikon sa tana da keken ɗinkin da dikkansu idan suka tashi aure sai Baba ya saya musu, wanda nata yake ajiye a daki ko hada mata keken ba a yi ba sabida Lawal da ya nuna baya bukata a wancan lokacin.*FITATTU BIYAR 2023 paid books:-*
1- *LOKACI NE na Fatima Oum Mumtaz*
2- *FARGAR JAJI na Aisha Abdullahi Yabo*
3- *WASA DA RAI na Fadeela Yakubu Milhat*
4- *ƘAYAR RUWA na Halimahz*
5- *KWANTAN ƁAUNA na Nana Haleema*_LITTAFI ƊAYA:- ₦500_
_LITTAFI BIYU:- ₦800_
_LITTAFI UKU:- ₦900_
_LITTAFI HUDU:- ₦1000_
_LITTAFI BIYAR:- ₦1200_
_VIP 2k._Za ku biya kuɗi ta wannan account...
*6314170140*
*FIDELITY BANK*
*SA'ADIYYA ZAKARIYYA HARUNA*sai ku tura da shaidar biya tare da sunan littafin da kuke biɗa a wannan number....*Oum Mumtaz(09061794195)*
katin waya zaku tura hoton MTN da sunan littafin ta wannan number...*Milhat(07083818353)*
*ƳAN NIGER KU TURA DA KUƊINKU TA Mkoudi 89356025 airtel, SANNAN KU TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAMBA...Aisha Yabo(08162576936).*
_LITTAFI ƊAYA:- 350f_
_LITTAFI BIYU:- 600f_
_LITTAFI UKU:- 650f_
_LITTAFI HUƊU:- 750f_
_LITTAFI BIYAR:- 850f_'''ƳAN KASUWAN DA ZA'A TALLATA MAKU HAJOJINKU DOMIN KASUWANCINKU YA ZAGA IN DA BAKU YI ZATO BA, TALLAN YA KASU KASHI-KASHI:-'''
*_TALLA A KOWANNE PAGE NA BOOK 500, 5pages2k, Complete Book 10k._*
*_•TALLA A VEDIO NA YOUTUBE 1500_*
*_•TICTOK 1500_*
*_•INSTGRAM 1500_*
*_•FACEBOOK 1500_*
*_•WHATSAPP STATUS; 24hrs500, 48hrs1k, 72hrs1500, 168hrs3500._*'''ku tura da kuɗin ta account numbern da ke sama sannan ku tura da shaidar biya haɗe da details na abin da kuke so a muku talla akai ta wannan lambar...NanaHaleema(09030398006.)'''
*Youtubers da suke son mallakar littafanmu domin ɗorawa a channel sai kuyi magana a wannan lamba...Halimahz(07018098175).*
MUNA MARHABAN DA KOWA CIKIN MUTUNTAWA, A ISO LAFIYA🤩
*Godiya tare da adu'an fatan alkhairi ga duk wanda ya siya littafin Fitattu Biyar...son so fisabilillah😍*