🙋🏻♂MAI NASARA 🙋🏻♂
(A book of true love story)
Nah
Marubuciyar ZamaniNABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)Email.....
nabilalady5@gmail.com
Facebook...Nabeela LadeeyPage 170 ➡ 175
Washe gari koda suka tashi atare suka fita masallaci. Baffajo da Maina da suka gansu sai da sukayi mamaki. Baffajo ne bayan an gama sallah suna gaisawa yake tambayar su ko a wajen Baffa Barkind'o suka kwana? Baffa Barkind'o yace ai kuwa nine nace amun kwanan bankwana kasan yau Mai Nasara a gidanshi zai kwana.
Murmushi Maina yayi aranshi yace lallai kama kwanan bankwana sukayi maka, dan kai dasu iya na yau ne kawai. Mai Nasara yace Hamma jiya ba'a tashi wasa da kai ba kuma. Maina yace wallahi kuwa, ina cikin kallo wani abokina da mukayi makaranta dashi ya kirani akan yazo, shine fa naje muka gaisa, mun dad'e dashi muna fira kafin muka taho dashi dan yana so yazo yaga wasan, muna zuwa kuma muka iske an tashi, shine yace wucewa zaiyi.
Majidad'i yace gaskiya kallo ya barka. Baffajo yace amma yau dai ai baza'ayi komai ba ko? Mai Nasara yace Baffajo ai ya isa haka kuma gara kowa yaje ya huta. Murmushi Baffa Barkind'o yayi yace kai dai fad'i gaskiya.
Baffa Lamid'o ne ya iso wajen su, nan suka gaishe shi shima ya gaishe dasu Baffa. Majidad'i yace Baffa jiya kuma sai kajimu shiru ko? Dariya Baffa Lamid'o yayi yace ai dama nasan jiya bazan samu 'yan fira ba shiyasa kawai muka kwanta.
Mai Nasara yace ai Kaku's nasan sai tayi k'orafi akan rashin zuwan mu. Majidad'i yace ai Kaku's akwai son labarai. Baffajo yace dama tunda lokacin biki yazo ai dole kowa yayi hak'uri har sai komai ya wuce sannan.
Tab'e baki Maina yayi yace Baffajo nidai nayi gida kafin gari ya k'ara wayewa nad'an runtsa. Baffa Barkind'o yace ba dai zaka dena wannan baccin asarar ba ko? Nasha fad'a maka baccin bayan asuba baccin asara ne, gara kazauna kayi karatu ko kuma kayi lazimi. Sosa kai Maina yayi yace zan dai na Baffa Barkind'o. Baffa Lamid'o yace ai gara adaina, sam baida amfani.
Nan suka wuce suna fad'in bara mushiga ciki. Baffa Barkind'o yace shikenan har kun tafi kuma? Majidad'i yace Baffa wani aiki zamuyi ne. Baffajo yace aifa, aiki ya samu.
Kai tsaye gidan Baffa Lamid'o suka wuce. Zinatu (Kaku's) tana kok'arin dama fura suka shigo, Majidad'i ne yace haba Kaku's, yanzu haka zanyi aure na kaiki gidana kirik'a tashi tun kafin gari yawaye kina damun fura? Murmushi tayi tace ja'iri, ko Uwarka Ammah da fura take karyawa duk safiya, lokacin tana yarinya tana tashi furarta tana gefe.
Dariya Mai Nasara yasa yace Kaku's ki rabu dashi, ko budurwa baida ita yake maki maganar mata. Kaku's tace ka barshi inaji da Khalcume zan had'ashi. Turo baki Majidad'i yayi yana fad'in haba dai, ai Khalcume tamun k'arama, kibar ma fad'i kada taji ta rainani.
Dariya sosai Mai Nasara yasa yace amma wallahi Kaku's kin iya zab'i, kinga dole yarik'a bani girma. Majidad'i yace kunga kudaina fad'in wannan maganar tun kafin Yusuf ya jiku, sanin kanka ne shine yake sonta.
Kaku's tace lallai abu yayi dad'i. Majidad'i yace amma fa kisama bakinki sakata koshi bai fad'a mata ba, yace sai ya kammala karatu sannan. Kaku's tace ai kaima kasan bana cikin masu surutu, sai dai muyi fatan zuwan lokacin. Mai Nasara yace tashi muje naga kana had'iyar miyau kuma ba baka zatayi ba. Majidad'i yace Allah ya kyauta nasha Fura tun da safe. Fita sukayi suna dariya.
Haka suka zagaya duka gidan suka gaishe da matan gidan, daga k'arshe suka nufi wajen Hajjo. Sun dad'e suna fira har abinci acan sukaci tare da Maina sannan suka nufi b'angarensu sukayi wanka saboda abokansu duk sun taho na nesa saboda d'aurin auren na k'arfe biyu ne.
*** ****
Da misalin k'arfe biyu dubban jama'a suka taru suka sheda d'aurin auren Yazeed Chibad'o da Falmata Garba. Sosai d'aurin auren ya had'a mutane, idan kaga fuskar Mai Nasara alokacin bakinshi baya rufuwa.
Maina kuwa ba'a d'aura auren dashi ba, yana nan dai har kowa ya hallara, babu wanda bai ganshi ba dan duk sai da ya gaisa da mutane, shine ma yaja Mai Nasara har ya zauna, akusa dashi ya zauna Mai Nasara sai farin ciki yake yana fad'in Hamman shine zai badashi. Dai-dai lokacin da za'a d'aura auren Maina yace ma Mai Nasara ga wani abokinshi can yazo bari yaje ya matso dashi, idan kuma cunkoso ya hanashi dawowa zasu tsaya daga baya kawai. Mai Nasara yace to Hamma.
Fita yayi daga cikin mutanan ya shige motarshi yabar wajen, dan alk'awari yayi bazai tsaya a d'aura auren Falmata da wani ba kuma ace yana wajen dashi za'a shafa fatiha. Tafiya yakeyi hawaye suna bin kuncinsa saboda rad'ad'in da zuciyarshi take masa.
Har aka kammala d'aurin auren sannan ya dawo, babu wanda yasan baya wajen, sai dai glass yasa a idonshi saboda idon yayi ja alamun anyi kuka, duk wanda ya tambayeshi sai yace k'waro ne ya faad'a masa a ido. Haka yayi ta yak'e yana gaisawa da mutanan da suke masa murna. Bayan da aka wuce wajen cin abinci ya samu ya nufi gida.
Babu kowa dan Hajjo tana can wajen mutane, d'akinshi ya shige ya kwanta saboda wani zazzab'i ne ya rufeshi. Wayarshi ya d'auko ya kira Falmata. Alokacin tana saman abun sallah ta gama nafila, dan tun lokacin da taga lokacin d'aurin auren yayi da tayi azahar kawai ta fara nafila tana mai godiya ga Allah.
Wayarta taji tayi k'ara, tana dubawa taga Hamma Maina ne, murmushi tayi aranta tace yanzu kam dole ka hak'ura, kaga zaka cigaba da kallona amatsayin matar k'aninka. Kamar bazata d'auka ba sai kuma tace kila shima ya manta komai yanzu ya kira ne saboda wani dalili.
Wayar tana sake k'ara ta d'auka. Ajiyar zuciya Maina ya saki wasu hawayen bakin ciki suka zubo mashi. A hankali Falmata tayi sallama, jin shiru tazo kashe wayar. Da sauri yace wallahi kika kashe mani waya zanzo na fallasa komai kowa yasan cewar ina sonki, kinga zan lalata ma Yazeed farin cikin yau, amma idan kika tsaya kika saurareni zan fad'a maki magana ne na k'yaleki saboda nasan ayanzu kin haramta agareni, tunda k'anina ya samu nasarar aurenki na hak'ura na barmasa ke, kuma bana fatan ki nuna masa na soki domin gudun b'acin ranshi, yanda baya son b'acin raina nima bana son nashi.
Ajiyar zuciya Falmata tayi jin abinda ya fad'i. Gyara kwanciya Maina yayi yace Falmata shikenan na rasaki har abada, na soki kamar raina, amma gashi Allah yasa ke ba matata bace, ni musulmi ne, dole kuma na yarda da k'addara, dan haka daga yau na hak'ura da ke, zan cigaba da kallonki amatsayin matar Yazeed wanda muka sha nono d'aya dashi, amma zansha wahala kafin sonki yabar zuciyata, sai dai zan cireshi ta k'arfin tsiya, zan maidashi akan Hajjota, na barki lafiya asaha amarci lafiya.
Sauke wayar tayi jin ya kashe, tausayinshi taji dan taji kamar hada alamun kuka yakeyi. Tab'e baki tayi tana fad'in ka taimaki kanka, domin Falmata ta Mai Nasara ce har abada. Nan k'anwar Ummanta tazo ta jata suka shiga ciki domin ayi mata wanka.
**** ****
Sai bayan isha'i aka d'auko amarya, 'Bangaren Baffa Barkind'o aka fara kaita, alokacin yana kinshingid'e yana jan carbi dan sam baya jin dad'in jikinshi, gashi dai ranar farin ciki ce amma baya jin farin cikin saboda yawan fad'uwar gaban da yakeji.
Baffa Lamid'o kanshi sai da ya fad'a mashi haka, cewar shima haka kawai yakejin fad'uwar gaba. Anan Baffa Barkind'o yace su cigaba da addu'a, koma menene insha Allahu Allah zai canza shi zuwa alkhairi.
Bayan da suka zauna anan yayi mata nasiha, sannan yayi masu fatan alkhairi suka nufi b'angaren Baffa Lamid'o da ita, acan ma addu'ar yayi mata sannan suka fito, wajen Baffajo sukaje daga can suka zagaya da ita wajen mutanan gidan.