💞PRINCESS JAWAHHIR 💞Wattpad
Mk_princess✍
1⃣6️⃣➖2️⃣0️⃣
Sunana Maryam Youssouf Tafeeda.... Babana Youssouf Tafeeda Oumarou dan kasar Niger ne cikin damagaram..... mamahna Ayishah Abraham Hakim ita yar Ethiopia ce Addis Ababa city dake garin Ethiopia Ni kuma na tashi a abuja gidan mu dake gwarinfa nan nayi rayuwa tundaga yarinta ta har na kai time din da na fara zuwa schl daga ni sai mamah na da daddy sai nanny na me suna baba jummai tunda na tashi nake ganinta a gidan mu ita take yin shara da goge goge mamah na kuma tayi girki ta kula dani komai mama na ce ke min mamah na ba karamin sona take ba ko ciwo nake tare mukeyi idan naki cin abinci haka zatai ta damuwa kuma ta kasa cin itama bata son ganin bacin raina daddy na kuwa babu abinda ke bata mai rai irin jin kuka na iyayena na sona matuka kawayena biyu kachal khausar da hidaya wanda suke neigbours din mu kuma tundaga nursery school har secondy da na gama NTIC dake nan abuja mun zama family friends dasu...
Sai Aminin daddy Alhaji Mahmoud da matarsa hajiya hadiza da yayanta ummi da khalifa daga hajiya hadiza har yayanta basu da dabi'a me kyau masamman ma khalifa danta da yake mara tarbiya ga shaye shaye shiyasa mamahna bata sakar musu ganin haka yasa suma basa zuwa gidan mu amma alhaji Mahmoud kullum yana gidan mu dashi muke dinner kullum....
ina rayuwa cikin farinciki da hutu abu daya ne ya fara damuna daga lokacin danayi wayo friends dina suna yawan zuwa garinsu kausar yar kano ce Hidaya kuma yar bauchi ce lokacin zuwa lokacin suna tafiya garinsu hutu su da family su amma ni daga daddy har mamah babu wanda ya taba cewa zai kaini Niger ko Ethiopia sai dai muyi ta yawo kasashe ni kuma idan su hidaya sun dawo sunzo gidan mu suyi ta bani labrin family dinsu da kakaninsu abin na burgeni idan suka tambayeni me yasa bana zuwa wajan kakanni na sai nace musu daddy yaki kaimu a haka har muka gama secondary school na samu first class dama kuma daddy yamun alkawarin zai kaini UK na yi karatun medicine dina a chan inata jin dadi ban taba tunanin daddy zai bar business dinsa da mutanensa mu koma UK ba kawai dan nayi karatu wannan abin ya karasamin san iyayena matuka haka mukai sallama da kowa muka tafi UK a nan muka hadu da Yaya SULTAN wanda ya Zane min kamar blood brother duda dai ina ganin yana takura min amma yadda yake kula dani ina jin dadi kuma yadda yake ma iyayena yasa na kara ganin kimarsa a idona sosai ....
Munyu 3 years a UK wata rana na samu mamah na Yaya SULTAN yace zai zo Nigeria nace zan bishi yace Aa mamah ma tace aa sai nace mata to ni ina so a kaini daya daga cikin family na ko niger ko Ethiopia hakan da na fada yasa mamana damuwa har tayi dan fushi dani hakan ne yasa na damu na same ta a daki tana zaune a kan gado na zauna kusa da ita ....
Nace mamahna fushi kike dani hararar ta tayi sai Kuma tayi murmushi....
Ganin tayi murmushi rungume ta tayi tace har naji dadi i though fushi kike dani dagowa nayi na kalli fuskarta kawai sai naga tana hawaye cikin tashi hankali nima na fara kuka nace mamah me ya faru me yasa kike kuka goge hawayenta tayi murmushi tayi ganin yar ta cikin tashin hankali kamo hannunta ya tace ba komai baby....Da sauri tace no mamah something is happen ban taba ganin kinyi kuka ba fa mamah saboda nace zan je Nigeria ne kike kuka wlh na fasa mamahna please stop carrying ta fada tana kara goge mata hawayen dake zubowa a fuskarta....
No isnt like that baby ina so ki nitsu ki saurareni nasan kema abun yana damunki nasan kina so kisan dalilinmu na kin zuwa garin mu daga ni har daddy ki bawai bama san ganin family dinmu bane aa mum fiki san mu gansu amma akwai wani sirri da muke boyewa wanda bazamu so ki sanshi ba....
maryam....
Da sauri na dago na kalleta jin ta fadi sunan ta bata kirana dashi ganin damuwar dake fuskarta ya kara daga min hankali sai na fashe da kuka ..
Murmushi tayi tace relax mana baby meye na kuka ki tsaya ki saurare ni in ba haka ba kuma tashi ki barmin kin San I really don't like it, stop it ta fada tana bata rai...
Hannu tasa ta goge hawayen fetace am sorry...
Good zan baki labari na da yadda babanki ya aure ni amma bazan baki labarin babanki ba saboda wani dalili...
Da kai kawai ta amsa...
Ajiyar zuciya mamah tayi tace ni yar Ethiopia ce kamar yadda kika Sani babana me arziki ne ya kasance kamar yafi kowa arziki acikin yan uwansa da suke dukansu mata kuma shi daya ne namiji hakan ne yasa yan uwansa mata suke ganin kamar shi ya gaje dukiyar Grandfa dina hakan ne yasa basa jituwa da yan uwansa du abinda yayi musu basa gani haka yake hakuri da halinsu har ya auri Ammina auren Ammina ma saida ya fuskanci bacin rai sosai sbd amina takawa ne sosai gata maraimiya dan grandma tace bazai aure ni ba yar uwarsa zai aura grandfa ne ya hana hakan faruwa aka auri mamana ta haifeni da shekara 4 ta rasu babana ya shiga tashin hankali bayan rasuwar mamana kakana ya rasu ganin haka grandma tace to ya auri wadda take so haka aka auri matar babana wadda ta wahalar da rayuwata basu dade da aure ba ta haifi kanwa ta sahfa Bayan haihuwar sahfa babana ciwon zuciyar da ya dade a tare dashi tun mutuwar Ammina ya tsananta lokacin ina 7 years ya rasu duda ban san dacin mutuwa ba amma rashin babana ya daga min hakali sbd shikadai ne yake sona family shi gabadaya basasona bare matar babana da ta zamar mim dodo bayan mutuwar baba na shiga takura ba rami ba wadda yan uwansa da mamarsa ta zo musu abin farinciki dan sun hau kan dukiyarsa sunyi daredare ba batun raba gado matar babana kuwa wadda take cousin a wajansa haduwa akai da ita suka ita yadda suke so inda take zaune a gidanku ita da yarta sai ni da na zama baiwa a gidan hatta makaranta saida aka chanza min kuma ita kanta makaramtar arzikin abokin babana ne yasa nake yinta badan shi ba da karatun ma bazanyi ba haka rayuwa taita tafiya sahfa ita ce yar gata ni kuwa banda azaba babu abinda nake sa da bauta ina da 16 grandma ta mutu bayan mutuwar ta ne yasa kowa ya watsar dani dan matar babana ma cewa tayi ita tagaji da rikon yar da ba tata ba dan badan tana da alaka da babana ba babu abinda zai sa ta reke yar kishiya kishiyar ma me farar kafa a daddafe nayi shekara biyu a lokacin na gama secondry schl wata rana ranar da bazan taba mantawa ba ina dakin masu ayki wanda tunda babana ya mutu aka maidani bq din gidan mu ranar babu kowa a gidan sai naji alamar bude get jin anshigo da mota yasa na fito dan a tunani na baki mukayi sahfa na gani ita da wani sun shiga cikin gida da mamaki na bita cikin gidan dakinta na sameta ita da wani suna aykata ba dai dai ba da sauri na dawo jikina na rawa juyawar da zanyi sai naga matar babana mun yi Karo tsoro ya kara kamani Mari na tayi karar Marin ne ya fito da sahfa wadda yanayi da ta fito ne ya firgita matar babana Cikin tashim hakali ta kara hango namijin da ke bayanta zuwa yayi ya wuce ya daga ma sahfa hannu daga mai tayi ita ma ta juya ta koma ciki ganin haka yasa dukanmu muka saki baki tsawa ta daka min tace na bar wajen jiki na rawa na bar wajan ina zuwa daki mayafi na, na dauka na tafi gidan abokin babana na same shi ina kuka nace ni dai zan dawo gidan sa da zama ay ban gama fada ba matarsa tace aa sbd dama kawar matar babana ce itama ba sona take ba haka ya bani hakuri na koma duda ban gayamai abinda ya faru ba yau ina komawa gida na samu matar babana tana jirana ta min duka tace naje na tona ma yarta asiri na rinka rantse mata ban gayama kowa ba tace idan ma na fada zaidai ni abun kunya ya sama amma yarta dai abin kunya bazai same ta ba.....