7️⃣1️⃣➖7️⃣5️⃣

174 14 0
                                    


💞PRINCESS JAWAHHIR 💞

Wattpad
Mk_princess✍

7️⃣1️⃣➖7⃣5️⃣

Kawai sai yaga ta dan runtse ido ta bude ta kalle shi kamar me koyaon magana tace da zafi fa....

Ay kamar wanda akai ma albishir da aljanna ya wani rikice da sauri ya kama hannunta yace so sorry baby da zafi...

Kai kawai ta gyda mai....

Wata ajiyar zuciya yayi turo kofar akayi S I ne ya shigo yace dama nasan kana nan kamanta kanada cs ne anje office dinka baka nan...

Kallon S I yayi da murmushi yace Alhamdulillah baby ta min magana...

Kallon sa kawai SI yayi girgiza kai a zuciyar sa yace Allah sarki bawan Allah ya kamu har wuya bai sani ba zuwa yayi gabansa ya dafa shi yace haba maza kana abu kamar ba dr ba ganin bata magana ay dama ba wai ta dena magana gaba daya bane kuma dan tayi magana bawai zai zama sabon abu bane any way Alhmdllh haka ake so dama kuma in sha Allah komai zai zama daidai....

Kuma dama ina so na gayama result dinta na ECO da ECG da mukayi Alhamdulillah shima mun same improvement sosai Dan haka Dan Allah ka rage damuwa abokina be a man mana haba namiji ya hada yana Dan tsokanar sa....

Murmushi kawai yayi ya juya yana kallon ta kofa aka bude su khalil ne suka dawo khalil ne yace basaraken dr number ka ta fito ana nemanka kai naga alama idan kana gaban babyn nan taka baka ji baka gani ya fada da sigar tsokana....

Dariya salma ta ke kasa kasa harararta yayi yace meyasa bakya san yi mata hira...

Zare ido tayi tace yaya hira kuma bayan kasan bazata kula ni ba bama zata saurara ba shiyasa nikuma sai naga kamar ina takurata idan ina mata magana bata ko kallona bare ta nuna tanajin me nake cewa..

Nasani amma gashi ni yanzu tamin magana kuma ta amsamin da na mata magana....

Da expression tace da gaske me tace maka cikin jin dadi yayi murmushi yace tace min da zafi ya fada yana mike wa kallonsa kawai suke dan su basu gane me yake cewa ba ganin yadda suke kallonsa sai ya basu labarin yadda sukai da ita khalil yace Alhamdulillah wannan ay abunda muke nema ne ya samu gaskiya ne basaraken dr salma ki rinka kokarin yi mata magana ko bazata amsaki ba wata rana zata amsa kai kuma oga tunda an samu cigaba sai ka rinka kokartawa duda dai naga patiant din nan taka tana so ta hanaka aykin ka....

Murmushi kawai yayi ya fita be basu amsa ba.....

Wannan kenan 📝

✴✴✴✴✴✴✴✴✴

Meerah ta gama hada kaya yau jirginta zai daga abuja suna zaune a parlo mama tace ki bude kunnan ki da kyau ki jini in kinje mun gama magana da mommy ki a kayanki na hada miki da wani sako ki kai mata sanan meerah ki Kama kanki kinga dai yaron nan ta karfi akai masa ba a sanransa yake son auren nan ba duda dai Akwai abinda zamuyi kafin aure kuma zaki sha mamaki zai soki fiye da du wata mace a duniya ke dai du abinda mommy ki tace kiyi Kwai kiyi kinjini....

Cike da murna tace an gama hajiya fulani me babban daki wlh ina son ki uwata....

Dariya take tace ja'ira ba dole ki soni ba nima ina sonki diyata.. Tashi ki tafi karki makara idan kin isa ki kirani ki gaida mommyn...

Ma aykatan gidan ne suka kwashi kayanta aka kai mota driver ya dauke ya kaita airport jirginta ya daga abuja....

✴✴✴✴✴✴✴✴✴

Yau Aunty sadiya ta iso garin soyaki ita da yaranta muhd, Afrah, da Arif.. An dakko su daga airport suna zuwa place yaran da murna suka shiga bangaren ummah suna murna da murna ummah ta tare su sunata zuba mata suruta Aunty sadiya ce ta shigo tace yanzu kai Muhd ba zaka dena wannan halin ba ji yadda ka barni ina ta neman waya ta a mota ashe kai ka dakko min ko bani wayata....

          

Turo baki yayi yace sorry Ammi ina game ne fa harararsa tayi ta karbe wayarta ummah dake kallon su tace to sarkin yiwa yara fada kawai kin shigo min daki da fada da murmushi ta kalli ummah tace Allah ummah Muhd ne bayaji ya maida min waya kamar ta wasan yara ta fada tana zama a gaban ummah tace ummah barka da yamma...

A'a ni bazan amsa ba saida kika gamai wa mijina fada zaki zo kina min wata gaisuwa ta fada da tsokana...

Dariya Aunty sadiya tayi tace tuba nake ummah na nan suka gaisa nan danan hadiman gidan suka zo suna kwasar gaisuwa aka ciki musu gaban su da fruits da kayan ciye ciye sai jin dadi suke...

Afrah ce tace ummah ina Aunty salma tana dakinta bara naje nace mata munzo kuma da ita zamu koma...

To aku sarkin surutu Aunty taki bata nan dawo ki zauna inji ummah..

Aunty sadiya ce tace ummah ya mai jikin kuwa...

Cikin damuwa ummah tace da sauki amma dai yarinyar nan tana bani tausayi tana jin jiki ga ciwo ga rashin iyaye...

Gaskiya ne ummah ni kaina da SULTAN ya min bayani ya bani labarin abinda ya faru na tausaya mata gata yarinya yar gata ta taso da rayuwa me kyau yanzu an gano danginta....

Inafa ay dole sai ta farfado zamu samu wannan sukunin yanzu dai ana bincike sosai akan kisan iyayenta kafin Allah ya bata lafiya a tambaye ta ko za'a samu wata sheda da zai saukaka binciken....

To allah ya bata lafiya su kuma Allah ya tuna asirin yasakawa iyayenta...

Ummah yanxu naga motar gidan nan a airport ta kai yarinyar nan yar kanwar mama meerah take kowa kinsan me tayi a gaba na ta cire abayar da ta dora akan riga da wandon ta cire abayar nan ta wlh kamar ba yar musulma ba ta faza gashin doki ke in kinganta bazaki kirata da sunanta ba...

Kuma tana kallona ta gane ni kuma tasan nima na gane ta amma ko kallo ban isheta ba wannan wace irin tarbiya ce ta fada tana jimama abin a ranta saida ta gama....

Ummah tace ummm ay ba wannan ne zai dameki ba sadiya cewa nayi kar a kagaya miki idan kinzo kyaji kinsan me martaba ya umarci babana da ya auri wannan yarinyar har ya tsaida rana dan jiya yake min bayani wai sunyi magana da mahaifin yaron sun tsaida rana wata 2 yanzu mahaifin yarinyar yace jibi za'a azo ay sa ranar...

Tunda ta fara mata bayani ta saki baki tana kallonta hawaye ne yazo idan ta kamar bazatai magana ba tace gaskiya ba'a yiwa ya SULTAN adalci ba ummah ya kamata a tambaye shi dama kinsan ko da dinma ita take haukanta take binshi take cewa tana sanshi kuma wlh nasan dan uwana bazai taba san mace irin meerah ba ummah dan Allah kiyiwa takawa maga.....

Bata karasaba ummah tace kul sadiya ya da hankalin ki kike wannan maganar umarnin mahaifinsa zaibi ko kuma san zuciyar sa zaibi kar na karajin wannan maganar dani dake dashi kanshi takawa yasan SULTAN baya son auren nan dan haka sai mu daukeshi kaddara Allah ubangiji ya sa haka shine mafi alheri ya kade mana fitina kiyi ta yiwa dan uwanki addu'a Allah ya shiga lamarinsa kinji.....

Jiki a sanyaye Aunty sadiya tace toh Allah ya shige mana gaba ya tsare mu daga sharrin makiya ummah ta amsa da Ameen ya Allah....

Abinci sukaci suna gamawa sai ga salma da khalil sun shigo a jere da sauri salma tazo ta rungume Aunty tace ammina sannu da zuwa wlh inata sauri dan nasan kun iso ta fada cike da farin ciki...

Aunty sadiya tace Allah sarki yata ta fari ya kike ya me jikin....

Alhamdulillah da sauki sosai dan yanzu tana magana idan tana son wani abu ma tana fada kuma idan ka mata magana tana amsawa sai dai a takaice.....

To allah ya bata lafiya....

Ameen suka amsa khalil ne yace to mu tunda baza'a kula mu ba bari na juya na koma inda na fito dama ina ayki ta takurani na dawo da ita gida..

Muhd ne yace uncle zan bika.... Arif ne yace allura zaije dariya dukayi gaba daya...

Dariya Aunty tayi tace haba na waje na bama haka da kai ya kk kuma yaushe zamu sha bikin ne kar kabari SULTAN ya maka wayo yadda kukai komai tare yanzu ma kuyi auren ku tare ya maganar ku tana nan ko kowa ta fada tana daga mai gira tana kallon salma...

Dariya salma tayi tace kai Aunty kifa mamana ce ta fada tana tashi daga wajan....

Dariya sukayi gaba daya har ummah dan sosa keya khalil yayi yace munyi magana sai ta karasa schl shi kuma sai zaiyi auren so zamuyi tare. .

Ummah ce tace kai ka kiyayeni so kuke ku zugashi ko naga alama to wlh kar inji kar ingani ta fada tana murmushi...

Aunty ce tace kana da gaskiya dan wlh ko bashida niyar kara aure sai na kara mai...

Ummah ce ta rike baki tace to sai ki kara mai tunda kece yar umn bari na tashi da wannan maganar taku inda abinyi ta mike ta dauki kur'anin ta, ta shiga daya daga cikin dakin kasa....

Zama khalil yayi yace yauwa sistar dama ina so muyi magana kan maganar SULTAN ne Wlh yana cikin wani hali abubuwan du sun masa yawa nan sukai maganar su ya mata sallama yace zai koma hospital...

To ka dubata zamu zo anjima da daddare kace ma ogan ina gaisuwa tunda ko a waya bazai kirani ya min sannu da zuwa ba....

Tsayawa yayi ya juyo yace Wlh sadiya kin raina mu kawai dan kinga kina da yaya uku ne to aure dai bashine girma ba ya juya ya tafi....

Dariya take sosai ta tashi ta hau sama ta shiga dakin da suke sauka in sunzo....

✴✴✴✴✴✴✴✴✴

A asibiti kuwa yana zaune a office har khalil ya shiga be sani ba saida ya dan daki table din shi a Dan firgice ya kalle shi....

Cikin damuwa yace haba SULTAN kasan abinda kakeyi ba dai dai bane ko ka zauna kai ta damuwa da tunane tunane bayan kasan me hakan yake jawo wa karinka ma kanka fada kar kaje kajama kanka wani ciwon kuma please .....

Ajiyar zuciya yayi yace wlh ni kaina bana so amma bazaka gane halin da nake ciki bane ga rashin lafiyar yarinyar nan ga case din iyayenta ga auren nan gashi ummah ma dazu kafin na fito danaje take gayamin wai jibi za'a zo sa rana za'a sa 2 month yanzu dan Allah kwata kawata ba wanda yake dubani na shirya ko ban shirya ba kawai anyi fixing date ba ruwan su da ni ya fada yana huce kamar wani zaki....

Dafashi yayi yace Comedown mana karka manta mahaifinka ne fa ya yanke hukunci ba wani ba ni abinda nake so kayi akan maganar auren nan ka zuba ido du abinda yace kayi kayi kawai ay yasan baka shirya dinba ya sa date din haka kayi hakuri ni nasan halin da kake ciki har wanda baka yadda kana ciki ba ma ni na sani kuma kaima zaka fahimta nan gaba kaidai kai ta addu'a...

Da aalamar tambaya yace ban gane wane hali ban yadda ina ciki ba kuna kai kasani.....

Murmushi ya masa yace ni nasani kuma na yadda ka kamu gam nawan....

Turo kofa akayi ummi ce wadda take kula da jawahhir tace ranku ya dade tuba nake hajiya jawahhir ce take ta kuka da tana yi a hankali da dr sulaiman yazo sai yace bakomai a barta tayi kukanta amma yanzu sosai take ihun kuk.....

Bata karasa ba nurse ta shigo tace sir your sister ay bata karasa ba ya miki suka fita gaba dayan su suka hanyar dakin da JAWAHHIR take....

✴✴✴✴✴✴✴✴✴

Tofa meya faru da JAWAHHIR din kuma ni MK ....

To amsar dai bana jin zan samu amsarta sai a next page in Allah ya bamu iko...

Jumma'@t Mubarak.

#more comment more typing 💞

JAWAHIRWhere stories live. Discover now