Chapter four

18 2 1
                                    

🤍MATAR SARKI🤍

By Aysha Rano✨

Wattpad@aysharano22

*In dedication to Aunty Sis*

Ina kuke manyan mata???
Ina 'yan gayu da 'yan kwalisa wanda sukeda burin gyara jikinsu????
Ina matan da suke fama da infection????
Kina buqatar kayan sawa na mata masu kyau kuma cikin farashi mai sauqi???
  Toku matso kusa yau ga Aisha Rano tazo maku da mafita,
ZAHRA'S_COLLECTIONS
DEALER IN ALL KINDS OF;
1.APHRODISIACS,(KAYAN QARIN NI'IMA); ZUMA ,HAKIN DAKA, SABULUN NURUL HUBBI, HADIN SARAUNIYA, TSUMI,DAHUWAR KAZA, YAN SHILA,DAHUWAR ZABI, BADAKARIYAR GUMBA...
2.APHRODIASICS SUPPLEMENTS
3.HIPS ENHANCEMENT SUPPLEMENTS
4.BREAST ENHANCEMENT SUPPLEMENTS
5.BREAST FIRMING SUPPLEMENTS
6.SLIMMING SUPPLEMENTS
7.WEIGHT GAINING SUPPLEMENTS
8.ANTI_AGEING SUPPLEMENTS
9.IMMUNE BOOSTERS SUPPLEMENTS
10. FAT BURNER SUPPLEMENTS
11. WHITENING SUPPLEMENTS
12. ⁠INFECTION SET

DIFFERENT KINDS OF TEXTILE FABRICS, E.G SHADDA, WRAPPER, MATERIALS, LAFAYAS,ABAYA AND MORE
DIFFERENT KHUMRA, SHU'UMAR KHUMRA, MAR'ATUSSALIHA KHUMRA, NURUL HUBBI KHUMRA, ANGEL KUMAR, BODY OILS.
PHONE NUMBER:09033446324/09079860649.

04

Bayan kammala musaffa masu jawabi sukayi jawabinsu daga nan kuma suka tafi zuwa ga maudhu'i na gaba wanda za'a kira kowacce daliba daga cikin masu saukar duk wacce aka kira zasu fito tareda guardin dinta zai karbi alkyabba a hannun daya daga cikin malamansu yasa mata alkyabbar a jikinta snn su sake yin gaba ya amsa Certificate da Allon saukarta shima a hannun wani malamin nasu ya bata da kanshi a daidai lokacin za'ayi masu hoto sai kuma a bashi mic ya dan fadi words of wisdom a kanta daga nan kuma sai kowa ya koma mazauninshi...tunda aka fara kiran daliban Sultan ya bude ido ya kuma kasa kunne yana kallo da sauraron duk abunda ke faruwa cikin ranshi yana regretting amincewa da yayi zai fita mata don baisan haka abun yake long process ba da ko kusa bai amince zaiyi ba saidai shi Tafeedan yayi masu...shi yanxu ta ina akeso ya fara yabon yarinyar da bai taba ganinta ba kuma wai dan rashin mutunchi har wani alkyabba ake saka musu sbd fitina irin na buzayen nan...shi bai taba ganin sauka irin haka ba koda ba zuwa yakeyi ba dai yasan ba kowacce makaranta keda fi'ili irin na wnn makarantar buzayen ba...juyawa yayi ya kalli Tafeeda daya shagala sosai yana kallon abunda ke wakana kawai saiji yayi in one word yace mashi"bazanyi ba"...da sauri Tafeeda ya juya yana dubanshi yace"ban gane bazakayi ba..what do you mean?"...kallonshi yayi sosai ya rungume hannunshi fuska a daure sosai yace"i said bazanyi ba...idan an kirata ka fita i can't do it"...yana rufe baki Tafeeda yace"haba don't say that plss...bayan ka sama yaron nan rai ya gama sakankancewa sai kuma yanzu kace ba haka ba?..haba kaji tausayin yaron mana ko don maraicinsu ka taimaka masu ba don komai ba sbd Allah"...kallon Tafeedan shima yake kaman zaisa kuka yace"but how do you expect me to just go and start touching a girl that i don't even know?..do you think this is a joke?"...da sauri Tafeeda yace"C'mon guy who said you gonna touch her?...kawai fa alkyabban zaka karba sai ka dan zura mata a jikinta shknn fa ba lallai ma sai hannunka ya taba jikinta ba Please!"...kallon you are not normal yakema Tafeeda yana kokarin sake mgn kawai sukaji muryan malamin dake kiran sunan dalibai ya mamaye wajen cikin mic yana kiran Fatima Zarah Muhammad...wani faduwa da gabanshi yayi da aka ambaci sunan zai iya rantsuwa tunda yake a duniya bai taba jin faduwar gaba irin wnn ba...Tafeeda ya marairaice gamida hade hannayenshi waje daya alamar roko murya can kasa yake ce mashi"pls plss plsss...pls Sultan ka taimaka masu domin Allah ba don wani abu ba Please i beg you"...lumshe ido Sultan yayi yanajin kaman yayi tsuntsu ya tashi daga wurin tsabar rudanin daya shiga amma babu halin yin hakan...sake kiran sunanta da akayi yasashi mikewa da kyar kamar mace mai tsohon cikin 'yan biyu wata tara ya fita daga tent din walking majestically like the king he will soon be...a daidai lokacin itama Zarah ke fitowa daga cikin nasu tent din kanta a kasa...Ammi dake zaune kusada Khalil tanajin an kira sunan Zarah ta shiga kokarin mikewa zata fita Khalil yayi saurin dakatar da ita da cewa sun samu wani yayan qawarta yace zai fita as guardin dinta...Ammi ta wara idanu tana kallon Khalil kmr ya fadi wani abun tashin hankali tace"Khalil😳...what did you do?"...da sauri yace"ni Ammi banyi komai ba kawai fa ta cema qawar tata Uncle dinmu baya nan yayi tafiya shine sai tace akwai brother dinta da yazo sai ya fita mata tunda kowa maza ne suke zuwan mishi"...kallonshi kawai Ammi take kamar bata yadda da abunda ya fada ba tace"but why did i find that hard to believe?...anya ba wani abu kaje ka aikata ba Khalil?"...a hankali yace"haba Ammi wani abu kuma?...idan baki yadda dani ba ki tambayi yayan aidai Kinga bazanyi mata karya ba"...girgiza kai kawai Ammi tayi bata sake cewa komai ba don gudun kar hankalin mutane ya dawo kansu kuma bataso abun ya wucesu don haka ta maida hankalinta ga Zarah da har ta karasa inda ake tsayawa bata daga kanta ba balle taga mutumin daya fita mata...kura mashi ido Ammi tayi daga nan inda take zaune tanaso ta gane waye shi din saidai duk kokarinta bata gane ba ta dai ga alama mai kwarjini ne sosai don daga nan inda take tana ganin hakan kuma bisa ga dukkan alamu daga babban gida ya fito duba da yanayin jikinshi dama suturar dake jikin nashi...karasawa yayi inda suke malamin ya bashi hannu sukayi musabiha snn ya bashi alkyabbar dake hannunshi...a hankali ya fiddo alkyabbar daga cikin Leda kaman yanda yaga sauran sunyi a baya sai yaji ya kasa daga ido ya kalleta sbd yanda har yanxu gabanshi bai dena squeezing ba...a daidai lokacin daya daga ido itama Zarah daidai wnn lokacin ta dago nata idon and to her biggest surprise taci karo da halittan da bata taba gani ba tunda take a duniya tsaye a gabanta a matsayin guardian dinta ga kuma alkyabba a hannunshi yana kokarin saka mata...sake bude ido tayi sosai tana kallonshi kaman yanda shima din ya kalleta nan take eyes dinsu sukayi collabo wanda hakan ya tilasta ma Zarah sauke nata idanuwan da sauri sbd wani abu mai kaifi da taji ya fita daga cikin idanuwanshi ya shiga nata...dan matsawa yayi kusada ita yana warware alkyabban Zarah ta sake daga ido ta kalleshi wnn karon sai taji kaman zata saki fitsari a wando sbd wani hadadden kwarjini da yayi mata...sai ta ga kaman ya cika duk wurin da kwarjininshi don haka tana sauke idon bata sake gigin dagowa ba saiji tayi a hankali ya bude mata alkyabbar ta bayanta aiko kmr jira take ta ware hannayenta ta zurasu a ciki shi kuma ya karasa zura mata tareda rufa mata hular jikin alkyabbar a kanta nan take wurin ya dauki kabbara da sowa...shiko Sultan yana gama Saka mata ya samu ya dan matsa kadan daga kusada ita dan yanda yakeji kaman faduwa zaiyi a wurin sbd wani abu da yaji sai zillo yake mashi a cikin jiki da zuciyarshi...bayan Saka alkyabba suka matsa table na gaba inda wani malamin again ya sake bashi Certificate da Allon saukarta shima ya sake juyawa inda take sai a yanxu ya samu kallon fuskanta da kyau ya kuma ga tanada haske sosai lokaci daya ya gama concluding cewa buzuwa ce don haka bai bari ya shagala da kallonta ba ya mika mata abubuwan itama ta Miko hannunta ta rike side daya ya rike daya akayi snapping dinsu a haka snn suka sakeyin gaba aka bashi mic wai ya fadi words of wisdom a kanta aikam Sultan yayi tsuru tsuru ya rasa abun fada...daga karshe dai yayi musu Salam snn ya dan yabi halayenta bla bla bla bla shi kanshi saida yayi mamakin yanda words din suka dinga fitowa daga bakinshi kmr dama ya rigada ya gama tsara speech din bayan ko sanin da wanzuwar yarinyar baiyi ba...yana gama speech din aka sake daukansu hoto snn suka rabu kmr jira suke Zarah ta kama hanyan tent dinsu shima ya koma inda yake zaune...yana karasawa ko gama zama baiyi ba Tafeeda da yake Allah Allah ya karaso ya wani cacimi hannun damanshi ya shiga shaking dinsu da nashi bakinshi a wangale kaman gonar auduga yake cewa"Superb bro...Superb...i never knew you can act this good...it was such a wonderful performance you know and....."kasa karasawa yayi sakamakon wani kallo da yaga yana binshi dashi ba shiri ya zare hannunshi daga nashi ya shiga danne daria don yasan yau fa mai rabashi da mutumin nan sai Allahu.

🤍MATAR SARKI🤍On viuen les histories. Descobreix ara