Part1

47 2 0
                                    

"Kamar ko wace ranar lahadin karshen wata, da karfe biyu na rana. "yau ma kafatanin iyalan" Turakin Zazzau, ne suka cika Babban dakin taron nasu dake asalin cikin gidan Turakin.
Kamar yacce yake a al'adar gidan manyan na zazzaune a kan kujerin dakin taron ya yin da kananun ke zaune a kan carpet.

  Gurin ya cika sosai wanda idan baka sani ba Sai ka zata taron biki ake saboda yawar jama'ar gurin. Saidai kuma kallo daya zaka yi musu ka fahimci cewa zuri'ar mutum daya ne, saboda tsantsar kama da suke da junansu kasan cewar auren dangi da suke a ahalin.
     banda tashin surutun tu sama sama ba abunda kake ji, sanarwar shigowan tsoho mai ran karfe akayi wato Alhaji Al_Dahir TURAKI. take gurin ya dauka wani irin shiru kowa ya shiga taita yinsa banda karar AC dake sauka a hankali baka jin komai.

A hankali kyakyawan dattijon ya yi sallama cikin gurin hadi da shigowa, cikin shigar sa ta rai da rai wato fararen tufafi, da daurin rawanin sa launin ja Sai idanuwansa da ke cikin farin glass dan karfafa ganinsa.
    A hankali ya nufi kujerar sa wacce take fuskantar kowa dake gurin haka kuma tafi ko wace kujera a gurin kyau da kawatuwa. take kowa a gurin ya mike ganin zai zauna.
Zama ya yi cikin nutsuwar sa da kamewa, ya dubesu  cikin muryarsa ta  dattijawa wacce kanaji kasan mamallakin ta yaga jiya kuma yaga yau.
Yace ku zauna, take kowa ya nemi guri ya zauna, gyarawa glass din idonsa zama ya yi, ya shiga karewa kowa da yake gurin kallo kafun daga bisani ya shiga bude gurin da addu'o'i ya karashe da sallama, kowa ya amsa.

A hankali ya shiga bayani.

Kamar yacce kowa ya sani duk karshen wata muna wannan zaman domin sake dorara zumunci a tsakaninmu haka kuma domin jin matsalolin juna da kuma kawo gyara a tsakanin. to yau ma ina mai Baku dama da kowa ya fada abunda yake ransa.

Alhaji Hamza, da kai zan fara"ya fada hakan yana kai dubansa ga babban dansa.

   Mikewa Alhaji Babba Hamza ya yi wanda kaf Familyn ke kira da Alhaji Babba. Sallama ya yi hadi da gabatar da jawabansa akan da ci gaban da yake so a samar a family, yana gamawa aka ci gaba da bawa kowa dama, duk mai abun fadi ya fada, daga karshe Hajiya Uwani ce ta mike domin yin nata jawabin, tun kafun ta fara TURAKI yaja numfashi dan yasan koma meye takeson cewa babu Alkhairee a cikinsa, dan ko wani lokaci zancenta akan abu daya ne, abu mafi soyuwa a ransa abunda yafi kauna a kaf ahalinsa haka kuma yakeji zai iya komai a dominsa....zancen Hajiya uwani ne yasa ya dawo da dubansa a kanta sabanin dazun da ya dauke kai..... Allah ya taimaki Turaki Khairath bata jin maganata da yawa a nan gidan sun sani amma kowa yana dauke kasan, haka kuma mata a gidannan basa Jan mota amma Dacta ya dau mota ya bawa Khairath, wanda abun khairath ya yi tsamarin da Sai ta wuni bata gida da sunan makaranta yanzun ma kaga ai bata nan kuma tana dawo akace ina ta Fito zata ce makaranta, sam ta rainani Turaki dan bani ce na haifeta ba. Kawai ta fashe da kuka, shiru gurin ya dauka na wasu mintuna kafun Hajiya uwani ta dora da cewa, kuma ma abun haushin yanzun khairath har maza take b.........wata irin  tsawa Turaki ya daka mata wanda ba ita ba kusan kowa da yake gurin saida ya tsorata, sosai fushi ya bayyana a fuskar Turaki, gemun sa ya dan shafa a hankali yace na rufe wannan zaman, Subhanakallahumma'wabi, hamdikh ash'hadu an_la'ilaha, illah anta Astagfiruka wa'atubu ilaih.  Yana gama fadar hakan ya mike ya fice daga dakin taron, take kowa ya shiga kama gabansa masu surutun abunda ya faru na yi masu zagin khairath na yi masu zagin uwani na yi wanda tsiraru ne masu yin hakan.

Kowa ya watse kaf, inda aka bar Dacta Muhammad Al_Dahir zaune yana sauke numfashi mai hade da takaicin matarsa ya rasa yaushe ne uwani zata yi hankali yaushe ne zata zama uwa a gun khairath yarsa kwaya daya tilo da ya haifa a duniya amma Sam matarsa bata kaunarta menene matsalar ne? Tambayar da ya yi wa kansa kenan wacce shi kansa yasan bashi da amsar ta.

       rike kansa da ya fara Sara masa ya yi, a hankali ya tashi ya fice daga dakin taron kai tsaye gidansa ya nufa wanda yake daya daga cikin jerin gidajen dake harabar, a parlour ya samu uwani zaune ta dora kafa daya kan daya tana kafa cup din juice a bakinta, wani mugun kallo ya watsa mata itanma maida masa ta yi cike da rashin mutunci, girgiza kansa ya yi yana kokarin shigewa part dinsa ta jefa masa magana, ya ce dai ta fandare ta zama tantiriya na fada kuma bazan fasa fada ba ehee. juyowa ya yi ya dubeta, Uwani ashe Jarabtarki da Allah ya yi da rashin haihuwa bai isa yasa kisan akwai wanzuwar mahalicci ba? Kuma kinsan cewa shine mai rayawa mai kashewa, haka kuma mai shiryawa ba, uwani ina jiye miki rayuwa fa..... to ai Dacta da dai haihuwa irin ta matacciyar matarka wallahi gwara na mutu ban haihu ba.

  Me ake da, da ko ya irin khairath?  wallahi na tabbatar ko kai da Turaki tsabar son kai ne yasa ba kwason a fadi kuskurenta, da haihuwar ya irin khairath gwara barinta wall........ To hell with you and ur damn fucking explanation..... karasa shigowa ta yi ta tsaya gaban uwani tace, bana shiga sabgarki and kinfi kowa sanin saka kai a sabgar mutane ba abu bane wanda ya dameni so please stay in ur limit... Khairath Dacta ya fada a kokarinsa na dakatar da ita, itama rai a hade tace, Dad please not today, for how long ur wife will keep insulting me and my mom? Am tired of all this na gaji........tana gama fadar hakan ta shige sashen ta, wani takaici ne ya sake kama Dacta ganin irin shigar da ke jikin Khairath din.
Ya ma rasa meye zai yi ko zaice kawai shigewa part dinsa ya yi. uwani kam banbaminta ta ci ga ba da yi hadi da tsinewa khairath din.

   "Kyakyawan dattijon kishin gide yake a kan kilishinsa ya yinda maganar Uwani ke ci gaba da dawo masa *Khairath bin maza* *take...!!!* sosai zancen ke amsa kuwa a kunnuwansa. Kaf zuri'a sa ya san cewa ba'ayi yaro mara jin magana kamar khairath ba saidai soyayyar yarinyar sam ta rufe masa idanuwa baya iya koda yi mata mummunan kallo duk da irin ka lubalen da aka samu kafun wazuwarta duniya, a ransa yana jin wata kila zunubansa ne yasa Allah ya jarabce shi da kaunar yar watakila rashin jinta shine hukuncin sa wata kila shine jarabawar da ubangiji ya zaba masa....! to amma har yaushe?

Komai sauke Numfashi ya yi, Allah ya sani yana damuwa da irin rayuwar da khairath take ta rashin ganin darajar manya ko ganin kimar su, amma baya taba zargin khairath da rayuwar bin maza, girgiza kansa ya yi ba dai a gidan Turaki ba... ya fada a sarari, daidai shigowar matarsa Fulani, da murmushi a fuskarta tace in sha Allah! dubansa yakai kanta hadi da sauke nasa murmushin yace ke ba da sanin mai nace ba ke da amsawa.

  Tana dariya ta zauna hadi da ajiye Bowl din hannunta, to ai ba Sai kace komai ba mai girma Turaki nasan koma me zaka fada Alkhairee ne.

    tashi ya yi daga kishingiden da yake, Fulani zancen khairath baya damun ki? ya fada yana zuba mata idanuwansa, murmushin takaici ta yi, zancen khairath waye baya damu Turaki?

Na rasa meye matsalar yarinyar, wannan Sam ba tarbiyar gidannan bace... ta karasa fada tana sauke hawaye, a a fulani banda dai kuka addu'a zamu yi mata Sai kiga Allah ya shiryata kuma ma ni ina ganin kuruciya ce... Kuruciya fa kace TURAKI? Khairath dince take da kuruciya? Yarinyar da.... daga mata hannu ya yi hadi da fadin ya isa haka, sanin da ta yi Sam baya ganin laifin khairath dinne ne yasa ta yi shiru da bakinta hadi da janyo bowl din da ta shigo da shi..... Ga abar fa na kawo ma, murmushi ya sauke, dadina dake kinsan mai ke faranta mun, to dai ga furarka ma sha Allah..... Ya fada yana Bude bowl din dukan su suna dariya.



********Hi Lovelies 😊how is it 😉I know u guy's will definitely like this journey hun ☺️  so the only thing u need to do is read vote comment and share so that nima n samu courage na rubutun uhmm😍

LOVE AND LIGHT ❤️

#love saga
#destiny
#family
#Turaki
#zaitun aur khairath

IDAN RANA TA FITO...Where stories live. Discover now