21

2.9K 42 10
                                    

✺ BAN FARGA BA ✺_* ✺✺✺ Farin Jini Writers Asso 21... Alhj Aminu yana da mata ɗaya Ummahani (Gran ƙenan) Asalin su yan damangudu ne amma kasuwanci ya dawo dashi otoukpo inda ya gina gida yana zaune da matar sa sun shafe shekara uku kafin Allah ya basu ciki murna a gurin Alhj Aminu ba'a magana domin yana mugum son ƴaƴa, haka ya ringa kulawa da ita har wata tara ranar lahadi da rana nakuda ya tashi da sauri ya nufi asibiti da ita tasha wahala sosai in da har an fara tunanin za'a mata cs, amma cikin ikon Allah ta haifi ɗanta namiji yan uwa da abokan arziki sun tayashi murna ranar suna yaro yaci suna AUWAL (baffa) kulawa sosai yake samu daga wajen mahaifanshi auwal nada shekara hudu Allah ya sake bata wani ciki wannan karon batayi murna ba sai Alhj kaɗai yake ta murna tunda ta samu wanan cikin kullun cikin fargaba taƙe domin ba karamin wahala taƙe sha ba, abinci ma bata ci bata iya cin komai Alhj aminu ya tausaya mata sosai haka ya bar kasuwancin sa ya dawo gida yana kulawa da ita shima auwal kullun yana makale da ita wani rana suna zaune da yamma lokacin Alhj ya gama yi musu girki domin shi yake musu komai lokacin kuwa cikinta na wata bakwai duk ta kunbura kai idan ka ganta saika tausaya mata domin bata iya tashi sai da temakonsa, sabida cikin ya rinjayi jikinta da kyar da motsa daga zaunen da take a hankali Alhj aminu ya matso gareta maka hannunsa tayi tana mai cije liɓe "nifa wlhy muje a cire min wannan cikin Allah mutuwa zanyi cikin ya isheni" cike da tausayawa yace kiyi hakuri ki kara tauriya saura lokaci kaɗan haka ya ringa rarrashinta da kyar ta kwantar da hankalinta domin ita tasan mai take ji, aikuwa koda cikin ya shiga watan haihuwa bata iya koda motsi kirki komai shike mata wata tara da kwana tara ta tashi da nakuda asibiti suka nufa wannan karon dai sai da aka mata cs domin ta kasa haihuwa tun daga ƙan HAMIDU (Dad) Allah bai kara bata haihuwa ba hankalin Alhj aminu ya tashi sosai domin yba karamin son ƴaƴa yake yiba, ita kuwa ko a jikinta domin ita tasan wahalar da take sha haka dai suka ringa rainon ƴaƴan su cikin so da kulawa kwatsan wata warana sun gama shirin barcin su har sun kwanta amma Alhj aminu bai yi barci ba sai kallon cellin yake yana jin wani yanayi tattare dashi a hankali ya miƙe ya nufin ɗakin su Auwal kasancewar sun girma sosai domin yanzun sun zama samari Auwal nada shekara 18, Hamidu kuma 14, zama yayi a tsakiyar su yana kallonsu ya jima yana kallonsu kafin ya shafa fisƙansu ya musu addu'a ya bar ɗakin. yana komawa ɗakinsu yaga mahaifiyarsu har yanzun barci take jawota jikinsa yayi yana mai sauke ajiyar zuciya jin ya matseta sosai ne yasa ta farka murya ciƙe da barci tace "Alhj lafiya baka kwanta ba" kallonta yaƙe sosai daga bisani yace "UMMAHANI wani yanayi naƙe jin kai na inna ji a jiki kamar bazan rayu tare da ku ba dan Allah koda bayan raina ki kula min da ƴaƴa na ki kulamin dasu sosai karki barsu suyi kukan rashi na ki kulamin dasu sosai" katse shi tayi dasauri. "haba ya zaka ringa faɗar magana haka zaka rayu damu baza barmu ba dan Allah kasa sani cikin wani hali mana kasan bazan jure rashin ka kusa dani ba" rumgume ta yayi a jikinsa sun raya wannan daren sosai sai da sukayi wanka kafin ya mannata da jikinsa har tayi barci shi bai yi ba, sai dai me washe gari da asuba ta riga shi tashi sai da tayi alwala ta ga dai har lokacin bai farka ba shida yake tashinsu amma har yanzun yana barci matsowa tayi inda yake tare da jan hancinsa a hankali tace "Abbansu ka tashi man karka makara" shuru tayi baiyi magana ba da sauri ta hau gadon tana taba shi amma sai taga ko numfashi bayayi hankalinta ya tashi sosai da gudu ta nufi ɗakinsu Hamidu tana bubbuga musu kofa a rikice auwal ya tashi ya buɗe kofar ganinta cikin wani yanayi yasa shi faɗin "lafiya kuwa umma?" cikin tashin hankali tace "babu lafiya zo muje ka gani" duk ta rikice cikin barci hamidu ya fara jin magana sama sama buɗe idonsa yayi dai dai lokacin da umma taja hannun auwal, suka nufi part ɗinsu da sauri ya miƙe ya bi bayansu. suna shiga ɗakin taga yananan yanda tabbarshi kuka ta saka tare da faɗin "auwalu duba min shi yaƙi magana tun ɗazun" tsaye kawai Auwal yayi domin ko ba'a faɗa masa ba yasan rai yayi halinsa, kuka hamidu ne yasa ta kallonsa a rikice "shikenan abba ya mutu..." iya abinda ta iya ji ƙenan sai farkawa tayi ta ganta a gadon asibiti yan uwanta na gefenta kowa fiskansa ciƙe da damuwa a hankali ta iya furta "inna MIJINA" auwal ne ya shigo da sauri ya karaso inda take "sannu umma kin tashi" kamshi tayi tare da faɗin "inna AMINU" lumshe yayi kafin yace "yau kwana takwas kenan da rasuwan abba" tayi kuka sosai da kyar aka rarrasheta. haka rayuwa ta ringa tafiya da daɗi babu daɗi har aka shafe shekaru da dama. lokacin har auwal sun gyara gidansu su mayar dashi na zamani domin sun kammala karatunsu suna kasuwanci shi kuma hamidu bai cika zama ba domin yana yawo kasa she daban daban a haka har auwal ya haɗu da Zainab a wani asibiti yaje gurin abokinsa nan yaga ta masa babu bata lokaci iyaye suka shiga cikin magana har aka yi aurensu hamidu bai zo ba sai dai yace zaizo yau gobe jibi haka har lokaci yaja sosai sai da umma tayi da gaske kafin ya dawo yana dawowa yaga zainab da ciki nan hankalinsa ya tashi yace shima aure zaiyi abin ya ba auwal dariya sosai har umma sai da ta masa dariya. nan ya mike ya fita ya barsu cikin gari ya shiga yana ta yawo wai shi yana niman mata haka ya ringa yi kullun yau daya tashi zai fita yazo gurin umma zama yayi tare da langwaɓar da ƙansa a jikinta "umma yau ki min addu'a Allah yasa na dace na samu mata nima nayi auren nan" sai da ta murmusa sanna tace "to Allah yasa a d dace" da murna ya fita zainab tace "uhmm kardai yau ma kayi kwantai" ta karasa maganar tana dariya gwalo ya mata kafin yace "aii yau zan dace domin zan fita da kafar dama kuma zan karatan lzaja'aa kinga dole ma nayi nasarar sace zuciyar wata yau ga kuma umma tamin addu'a hull" haka ya mata gwalo ya fita mai mimi zatayi in banda dariya sai da tayi dariya sosai umma ma na taya ta addu'a itama ta masa. yana fita bai zarce ko inna ba sai wani kanfanin abokinsa zama yayi suka sha hira sosai sai yamma likis sanna ya masa sallama yana fitowa tafiya yake cikin sauri tana duba jakarta bata ankara ba taji ta bige mutum jakarta ya faɗi a kasa a hankali ta ɗago tare da furta "yi hakuri dan Allah ban lura bane" sun kuyawa tayi ta haɗa takardunta har ta bar gunrin yana binta da kallo. ganin zata shiga motar ta ne yasa ya nufeta da sauri "ji mana am mata" cak ta tsaya ta kwashi mintu kafin ta juyo "pls ya sunanki" a takaice tace "maryam" ɗan murmushi yayi kafin yace "maryam farat ɗaya kin min sata" dafe kirji tayi tare da faɗin "subahanalillah satar me..." sai da abin ya basa dariya ganin duk ta wani diririce kamar zatayi kuka, "dont worry fa ba wani abu bane zuciyata kika sace wlhy i love u maryama" numfashi taja da karfi tana ajiyar zuciya sai kuma ta sunkuyar da ƙanta kasa maganarsa ne ya katse ta "kina sona?" shuru tayi daga karshe ma ta fara kokarin buɗe motar ta, "aii wlhy baki isa ba sai kince kina sona zaki bar gurin nan kinsan wahalan da na ringa sha ne" waiii abin dariya yaso bata aikuwa sai da ta dara kallonta yake domin dryr ta mata kyau sosai bai barta ba sai da ta amince masa nan ta faɗa masa gidansu numberta ya karɓe dan tsaban iya shege har da hoto ya mata wai zai nunawa matar yayansa" ita dai dariya taƙe masa a haka dai da kyar ya barta shima ya nufi gida. ko sallama baiyi ba ya faɗa gidan da ihu fitowa auwal yayi daga part ɗinsu yana faɗin "kai kai waye haka" ganin hamidu ne yasa shi faɗin "a a mai niman aure ko dai yau ma kwantai akayi ne" jin haƙan yasa Zainab fitowa da ɗan cikinta tana dariya umma ma fitowa tayi ta tsaya "a a tofa na yau ƙenan ɗan autar umma" cewar zainab . hararata yayi tare da kunna wayar sa. tasowa yayi ya kama hannun umma da zainab yace "kalleta beauty gsky na ita zaɓe" zainab tace "kai gaskiya tayi kyau inna kuka haɗu har ta amince zata kwashi Kwantai" kwace hannun umma tayi tana dariya nan ya shiga basu labari dariya auwal yake harda kama ciki. cikin lokaci kalilan akayi auren maryam da hamidu zaman lafiya suke yi sosai inda taƙe zuwa gurin aikinta Zainab dai auwal ya hanata duk wata Yana biyanta lokacin da Zainab ta haihu Maryam na d'aura i'donta Kan yaron taji duk duniya ba abinda take so kamar yaron shima Auwal hakane yafi kowa murna kamar shi aka ma haihuwar ranar suna yaro yaci suna Yusuf Yana kaiwa yaye Maryam ta d'auke shi har Zuwa lokacin Bata ta'ba ko batan wata ba sosai Mimi take tausaya Mata har aikin hajji sai da tayi tana Addu'ar Allah ya Bata haihuwa shuru ba labari har aka kwashe shekara goma Nan ta Kuma ta kuma d'auko yarinyar Yayarta tana riƙe da ita Maijidda i'ta momy suke kiranta inda suke Kiran Zainab da Mimi sosai take son haihuwa har Maijidda tayi Aure momy Bata samu ciki ba cikin ikon Allah lokaci d'aya Kuma sai gashi sun samu ciki da Mimi murna Gurin Yusuf da Dad ba'a Magana cikin na i'sa wata Tara abin mamaki Rana d'aya suka tashi da nakuda inda Mimi ta fita hayyacinta Momy Kan suma tayi domin Bata ta'ba zatan Haka haihuwar yake ba Haka aka nufi asibiti dasu Mimi ce ta fara haihuwa inda ta haifi yara tagwaye duka mata Amma Sam Bata cikin nutsuwarta allura barci suka Bata Bayan ta haihu momy kan sai da aka Mata C's domin ita ko kwakkwar motsi Bata iyawa an samu nasaran Ciro Mata d'a namiji Amma yaron bai zo da Rai ba sosai Dr Saddika ta tausaya Mata ganin yanda take son yara. Gashi ta sha wahala amma jaririn ba rai hak'an yasa ta nufi d'akin da momy take Nan ta tarar da Maijidda tare da Mai aikinsu da sauri suka ce “lafiya ya momy” hawaye Saddika ta share kafin tace “Hajiya Maryam an Mata C's sai dai d’an ba rai yanzun abinda nake so daku dan Allah zan d’auki yarinyar Mimi d’aya in kaiwa Maryam tunda dukansu basa hayyacinsu Amma ya zama sirri fa tsaka ninmu” Nan suka yarda Saddika ta d'auki d'aya daga cikin jariran ta kaiwa momy da sauri ta d’auki gawar na momy ba tare da kowa ya sani ba ta bayar aka binne.. Kwanan mimi uku ta farka momy kuwa sai da tayi kwana 14 kafin aka sallameta lokacin an rad'awa yar mimi suna Maryam i'ta Kuma momy nata Yusrah mimi tana kaunar Yusrah sosai sai dai i'ta Yusrah bata samu kulawar uwa ba domin mud'din momy zata fita office gurin mai rainonta take barinta hak'an na ta'ba ran mimi Gran tayi fad'a har ta gaji gashi shima Dad d’in baya zama yau Yana wancan garin gobe yana wannna garin. A Haka Yusuf ya ke d'aukarta ta shiga da i'ta d'akinsa tun tana yarinya yake wasa da i'ta tun Bata fahimta har ta fara fahimta daga lokacin ta fara janyewa daga garesa Amma kullun saiya yi yanda yayi dan ya damu biyan bukata da i'ta tayi kuka har ta gaji kullun sai Tama momy kuka in zata office Amma momy Bata tsayawa sauraronta. Wani rana tana kwance a d'akinta Bayan ta Gama kuka momy ta tafi Yusuf ya shigo ya rumgumeta a jikinsa da sauri ta mike jikinta na rawa domin ba karamin tsoronsa take ba ganin Yana cire kayansa ne yasa ta fita a gidan da gudu Gidansu kawarta Amina ta nufa inda ta fara jin nishi tun k'afin ta shiga d'akin tana shiga taga Amina tsirara ita da wata suna kwakular junansu i'hu ta sa tare da fad'in “Minaty meye Haka fisabidillah bana hanaki ba” da sauri Amina ta tashin tasa kayanta tare da Korar wanda suke tare kamata Minaty tayi kwace hannunta Yusrah tayi tana kuka “sorry kawata ki daina kuk'an na bari” Ajiyar zuciya Yusrah ta sauk'e Nan tace “wlhy kawata Zaman gidan mu ya i'sheni wlhy na gaji Yaya Yusuf Yana takura min sosai” sosai Minaty take rarrashin ta kullun in hak'an ya kasance gurinta take Zuwa domin wani i'rin so suke yiwa junansu Amina mahaifiyarta ta rasu Sai matar babanta Bata shiri da matar Baban nata domin tana muguwar matace Bata da i'mani hasali ma halin da take cikin matar Baban nata i'ta ta jefata. Wannna Kenan Mu dawo cikin labarin.....

BAN FARGA BA..Where stories live. Discover now