Chapter 9

8 2 0
                                    

        ASHE NI 'YAR TSINTUWA CE

*Daga Kundin ✍️📚✍️
*Alkhamis KSA*
Wattpad: @KhamisSulaiman
Whatsapp: +2348095933008
Phone no: +2348085871223

                     *page 17 & 18*

   Bayan Alhaji Ahmed da malam Buba sun kai Aisha gidan Alhaji Inuwa, suna zaune bayan sun gaisa.

      Alhaji Inuwa ya kalli Hajiya Sailuba, yace "Hajiya ki sa a kawo ruwan sha mana"

       Sai Hajiya ta tashi ta kalli Aisha, tace" Tashi kema muje ki kai kayan dakinki mana"

     Sai Aisha ta tashi su shige ciki Aisha ta haye sama ita kuma tasa mai aikinsu ta kaiwa baki ruwa sannan Itama ta haye saman wajen Aisha.

       Alhaji Ahmed yayi murmushi yace "Aisha kenan sarkin rigima!"

      Alhaji Inuwa yace "In kaji rigima ma daya kenan, ga shagwaba iri iri saboda ta samu uwa mai riritata"

       Alhaji Ahmed yace "Ai kaima kuwa ba baya ba wajen tarairayarta, ai duk ta gaya min, har cewa tayi ba don ku kuka gaya mata da kanku cewa baku kuka haifeta ba babu wanda zai gaya ta yarda ko duk jikinta kunne ne tace ko za'a shekara ana gaya mata ba zata yarda ba"

     Malam Buba yace "mu dai Alhaji babu abinda zamu ce sai dai muyi fatan Allah ya saka muku da alkhairi"

     Alhaji Inuwa ya jinjina kai yayi murmushi yace "Haba malam ai ba wani abu bane........"

      Malam ya tari numfashinsa yace "Kayya Alhaji! ai kasan hausawa sukan ce 'yaba kyauta tukuici to mu babu abinda zamuyi muku tukuici dashi daya wuce godiya da addu'a, kuma ma ai yabon gwani ya zama dole"

      Sai mai aikinsu ta musu ruwa da juice da kuma kofuna ta ajiye musu a gabansu bayan sun sha.

      Malam Buba ya kalli Alhaji Inuwa yace "Bayan haka kuma Alhaji akwai wata magana mai muhimmaci da zamuyi kafin mu tafi"

      Alhaji Inuwa yace "Ina sauraronku"

       Malam Buba yace "Kamar yadda ka sani addinin musulinci shine addini na gaskiya kuma ya umarci iyaye su dasu bawa 'ya'yansu hakkokinsu da suka rataya a wuyansu wadanda Allah (S.W.T.) ya sanar da manzonsa Annabi (S.A.W.) shi kuma ya kuma ya sanar damu, kusan duk hakkokin Aisha da suke kan iyayenta kunyi mata su face guda daya tak! shine aure. Aure dai shine mutuncin 'ya mace shine kama kamalarta, shine darajarta, mace duk iliminta duk kyawunta duk nasabarta duk dukiyarta duk gatanta, kasani mutuncinta da darajarta da kamalarta basa fitowa sai tana da aure. Don haka lokacin yayi da ya kamata a ce Aisha anyi mata aure, mun sauke sauran nauyin daya rataya a wuyanmu nata kamar yadda addinin musulinci ya shimfida mana"

      Alhaji Inuwa ya jinjina kai cikin alamun rashin jin dadi yace "Hakika na dade ina tsoron zuwan wannan rana, na dade ina tausayawa kaina idan wannan ranar ta riskeni ba don komai ba sai don irin son da nakewa Aisha. Hakika Allah ya jarabceni da son Aisha fiye da kaina da raina, shine nake ta gudun zuwan wannan rana gashi kuwa yau ta riskeni.........! "

      Alhaji Ahmed cikin yanayin tausayawa ya dafa shi yace "Kayi hakuri Alhaji Inuwa Allah da Annabi ne suka umarcemu da yin hakan......"

       Alhaji Inuwa ya dago kai ya kalleshi idonsa cike da hawaye yace "Nasan da haka Alhaji Ahmed! amma ina so kuyi min wata alfarma guda!"

     "Haba Alhaji ai kai ka wuce ka nemi wata alfarma a wajenmu mu kasa yi maka matukar bata sabawa Allah da Annabi ba"

      "Aisha tun tana karama wani  bai taba hadata da wani da namiji ba har ta kai su ga soyayya, ina son ku bani kwana biyu zanyi tunani akan wannan lamari kuma zamu yi maganar da ita abinda muka yanke zan muku waya na sanar daku"

ASHE NI 'YAR TSINTUWA CE Where stories live. Discover now