chapter 4

477 46 6
                                    


(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

🌹 HAR ABADA 🌹
(Forever)

LOVE & FRIENDSHIP

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

TELEGRAM: https://t.me/joinchat/VOW8-BwH_DjWH1YfVcFONA

WATTPAD: https://my.w.tt/4ZfEeBpVecb
OR
@ayeeshatmuhd

BY
UMMU NAJMA

DEDICATED TO
MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA

Wannan shafin naki ne ummu sultan(Ruqayya ikra)
Allah yabar qauna ❤️

My first novel
04🍎

1:33pm

Abdulrazak ne ya jasu sallah Dan sauran mazan duk sun tafi masallaci sallan juma'a, ana idarwa Fannah ko addu'a batayi ba ta qarasa dai dai kunnen Abdulrazak Wanda yake Yan addu'oin sa akunnen sa tarada masa

"Dan jariri Mai Shan nono Ashe an girma har an zama liman! Allah yasa ba karatun Shan nono ka mana chikin sallan ba😂

Takaici ne ya kamashi ya daga hannu ya maka mata duka a cinya

"Kan uba, ai wlh kayi kadan ka dakeni kaci banxa, duk wani iskanci da rashin mutuncin da kake fama dashi nawa ya taka naka.

Ta daga hannu ta dallah mishi Mari a fiska,
A harzuqe ya miqe zai dake ta Ummi tace
"kul, kul da wasa wlh
Ita ba sa'ar wasanka bace,
Daga ta maka magana sai kahau dukan ta sbd raini?
Tashi kabar Nan wajen"

A qufule ya fita Yana qunquni Kuma yasa a ransa cewa Koba yau ba sai ya rama double din abin da ta masa.

Garden ya nufa yasha iska sbd zuciyan shi ta huce .

Momy dake zaune kan sallaya ta yi tagumi ta daga hannu sama tace

" Allah Kaine Allah Wanda babu abin bautawa da gaskiya bayan kai, Allah nagode maka da kyautar da kamun ka qaramun, ka shiryar mun da khadeejah ta tafarki ma dai_daici ka nutsar da ita kaman sauran yaran sannan in roqon ka kasa mata salama da son zaman lafiya cikin zuciyan ta"

Zumburo baki Fannah tayi tace "momy meye haka Kuma?"

"uwaki ne haka, nace uwaki ne haka Dan qaniyar ki
Ace yarinya kwata kwata baki da Kan gado?
Tunda kika zo duk gidan nan babu Wanda baki tsokane shi ba!
Shikenan ke idan kina wuri babu zaman lafiya?
Haba kekuwa.
Ki gyara halayen ki wlh!"

Kara zumburo baki gaba tayi ta wuce kitchen bayan an tattara parlorn ta fito da plate din abinchi da glass din ruwa tadau yaron aunty Shaheeda Wanda yake ta qananun kuka Kuma tana da yaqinin yunwa yake ji ta zaunar dashi ta fara bashi abinchin a nitse.

Karar doorbell ne yamai da hankalin su ga qofa suna tunanin mazajen gidan ne suka dawo daga masallaci Intee taje ta bude qofar.

A harzuqe ya shigo kaman wani mayunwacin zaki ko sallama babu sauran ukun suna biye dashi abaya
Abbas ne babbar Dan aunty Zali Wanda yake kusan sa'anni da ya Abdallah,
Bayan shi Kuma wasu mazane guda biyu majiya qarfi Wanda ban sansu ba sai kuma aunty Zaliha uwar gayyan gaba daya.

Fannah kallo daya ta musu ta watsar ta juya taci gaba da abin da take yi.

"Ina shegiyar fetsararriyar take?"

Ya fada sai muzurai yakeyi yana huci kaman zai tashi da wuta

Sabodd girman parlorn saida yayi tafiya sosai kafin ya qarasa inda take zaune, Yana gwada ta da yatsa yace

HAR ABADA (Under Edition)Where stories live. Discover now