chapter 22

242 35 0
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

      🌹HAR ABADA🌹
          (bazamu rabeba)

       LOVE & FRIENDSHIP

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

Vote me on Wattpad @ayeeshatmuhd

      RUBUTAWA

      UMMU NAJMA
   
DEDICATED TO
MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA

22🍎

Da sauri ta tashi ta bishi part dinsa, ta same shi Yana zaune ya zabga uban tagumi
"Yaya what are you trying to do?"

"I also don't know lil sis, bani da wata hanya bayan wannan I'm so confused"

Tausayin shi ne ya kama Sahar , Bata taba ganin yayan ta cikin irin wannan yanayin ba, zama tayi kusa dashi tana kallon yanda idanuwan shi suka sauya kala zuwa jaa.

"Yaya idan ka yanke wannan hukuncin ka saka happiness din Feenah at stake, kasan ba zata taba amincewa da Kai ba she doesn't like you, pls ka canza shawara".

" I'm sorry Sahar but aikin gama ya gama dad ya riga da ya yarda Kan maganar auren Dan Haka idan har ina so na tsira da mutunci na
hakan shine kawai mafita gare ni".

Hugging dinshi tayi tana jin yanda jikin shi ya sake gaba daya babu sauran kuzarin da koyaushe yake tattare da shi
"Insha Allah komai zai yi dai_dai Yaya, fa Inna ma'al usri yusrah".

3:00pm

Baba ne zaune da dady ga imran da Yaya Muhammad da Yaya Saleem harda ucle Omar, Ahmad Kam bai samu zuwa ba saboda tun da Rana zazzabi ya rufe shi.

Dad ne ya bude musu zaman da addu'a sannan ya isar ma baba qudurin Ahmad, murmushi baba yayi yace
"Masha Allah haqiqa naji Dadin wannan al'amari, Kuma zanyi matuqar farin ciki idan wannan Abu ya tabbata sai dai inaso Amin wani alfarma guda Daya,
shi yaron ya nemi yardar yarinyan su fahimci juna idan har ta amince dashi shikenan na baku ita halak malak Allah ya Sanya alkhairi a cikin zaman su".

"Ameeen Yusuf na gode da irin karramawan da kayi min Allah ya bar zumunci".

" Haba Abdulmaleek mene ne abun godiya? Kamanta cewa duk wani abin da na mallaka naka ne, kana da iko akan komai nawa Kai Mai bada auren Nafeesah ne ko ba da sani na ba."

Bayan sun gama yanke shawara da murna Yaya Muhammad ya shiga ya sanar masu Ammi, albarka ta saka musu domin ita Bata da ta cewa, Bata taba yin jayayya Akan hukuncin da mijin ta ya yanke ba musamman Akan yaran sa tasan badai taba cutar dasu ba.

Mama wani haushi da bacin Rai ne ya turnuqe ta, ta Yaya da'ace wa'innan shahararrun masu kudin suce suna so dansu ya auri Feenah bayan jidda itace babba,
Mai yasa ba zasu zabi jini ta ba sai jinin Ammi , jidda tafi Feenah hasken fata Kuma tafi Feenah wayewa tasan ma wannan yin baba ne shi ya qulla saboda ya gwada ma duniya yafi son hafsat akan ta  to wallahi ba zata Sabu ba.

Ta dauki waya ta Danna Kiran hawas wanda ta tafi uwa duniya neman Ahmad dinta don tunda  ta saka idon ta akan shi ranar da suka hadu a super market ta fita yawon neman shi, har yau Bata ganshi ba Kuma Bata fasa ba, Saida kiran ya kusan tsinkewa kafin hawas ta dauka.

"Hello Mama Yaya akayi?"

"Jidda kiyi sauri ki dawo gida akwai matsala babba".

" Matsala Kuma me ya faru?"

"Wasu hamshaqan masu kudi ne dansu yace Yana son Feenah bayan gaki a gaba na, kiyi ki dawo musan abin yi"

Wani matsiyacin dariya jidda tayi tace
"ayya mama ki barta ta aure shi yanzu Haka ma bani gari naje abuja Nemo Miki sirikin ki me wani mahaukaciyar arziqi kawai idan ana nema na kice muntafi excortion daga school".

"Yauwa that's my girl Daman nasan kin fi wancan yarinyan daraja sai kin dawo"

" Yauwa mama sai na dawo bye"
Ta katse wayan.

Mama ta zauna tana wani murmushin cin nasara ita burin ta komai nata yafi na Ammi har tana imagining irin bidirin da zata yi a bikin hawas din ta idan ta Sami wannan guy din Abuja.

Washe gari 6:00pm Feenah ta shigo gida saboda wani mugun lecturer da ya riqe su duk da sanin cewa Friday afternoon ba'a lecture.

Bata Dade da shigowa ba aka Kira sallan magrib, bayan sun idar ne Ammi take fada Mata hukuncin da su baba suka yanke a Kan ta don already tasan da zuwan baqin baban sai dai Bata San su a fiska ba.
"Yanzu ki tashi kije ki shirya sunce bayan sallan Isha dai zo"

"Ammi yanzu kema kin amince da wannan bahagon al'amarin? Ta Yaya da'ayi mutum Bai taba ganin na ba Kuma yace Yana so na da aure?".

"To Feenah wannan Kuma Allah masani, nide abun da na sani shine wa'innan mutanen ba na banza bane Allah ya Sanya alkhairi kawai a ciki"

" Ammi idan bani sonshi fah?"

" Shikenan Allah yayi ba mijin ki bane, tashi ki yi abin da na saka ki bani son dogon tambaya".

Tana qunquni ta tashi tayi wanka ta shirya cikin lace light green dinkin riga da skirt tayi simple make up ta saka hijab tayi sallan Isha.

Tana cikin addu'an ta Hussain ya shigo ya zauna a gaban ta Saida ta shafa tukunna cikin nutsuwa yace
"Aunty Feenah baqon ki yazo Yana jiran ki a guest room din baba".

Sai da Ta ja guntun tsaki kafin tace mishi "jeka kace Mishi Ina zuwa"

Da to ya amsa ya fita, ita Kuma ta tashi ta daura dankwalin ta kafin ta fesa body spray kadan ta dauki veil dinta da phone ta nufi dakin da Ahmad yake.

Sallama tayi ta shiga, ganin fuskar abin da tafi tsoro a duniya yasa ta juya ta iba da Dan iskan gudu zata bar dakin..............🧚

Kuyi haquri please bani da lafiya ne sosai, duk yanda naso yin typing me yawa kasa wa nayi🙏

#Vote
#share
#comment pls.

HAR ABADA (Under Edition)حيث تعيش القصص. اكتشف الآن