chapter 9

377 37 2
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

    🌹 HAR ABADA 🌹
           (Forever)

     LOVE & FRIENDSHIP

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

TELEGRAM: https://t.me/joinchat/VOW8-BwH_DjWH1YfVcFONA

WATTPAD: https://my.w.tt/4ZfEeBpVecb
OR
@ayeeshatmuhd

     BY
       UMMU NAJMA
   
DEDICATED TO
MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA

Aisha isma'il Fannah ta gode da irin qaunar da kike nuna mata Fannah loves you too 😍😘

09🍎

8:10
Khaleel ne jikin ƙofar dakin fannah Yana ta knocking Amma taqi ta bude,Magiya ya fara Mata Yana roqonta ta bude qofan.

Sai da ta dauki kusan 30 minutes kafin ta bude.. idon ta yayi jaa fuskan ta yayi luhu_luhu saboda kuka, ta tsaya a gaban shi ta riƙe da ƙugu fuskan ta a tamke tace
"Mene ne?"

Iska ya furzar yace
" Haba cupcake me yayi zafi haka? Kina ta punishing kanki kinƙi cin abinci tun jiya Akan abun da bai taka Kara ya karya ba"

"What? Me kace? Shegiya fa aka cemin, she called me a bastard, tayi wa momy na qazafin zina, ta Kira Ummi na da tambadaddiya but kana Kiran shi abun da bai taka Kara ya karya ba?
Fine tunda ka zabi auntyn ka akai na I'm leaving sai kaje ku zauna tare."

Tajuya ta shiga ciki tana hado kayayyakin ta,
Binta yayi abaya Yace
"Haba Fannah daga mgn sai ki fara ƙoqarin tafiya, baki da lafiya fah please kisa wa ranki salama mubi komai a sann......"

Dakatar dashi tayi da hannun ta
"Babu ruwan ka da rashin lafiya  ta kabar ni na tafi na rarrashi momy na ko babu komai ita tasan daraja ta."

Marairaice fuska yayi cikin ƙosawa da musayar yawun da suke yace
"Faannahh ki saurare ni Mana duk wannan ba abun daga hankali bane, ki nutsu pls nasan abinda ta fada kwata_kwata bai Dace ba Amman Dan Allah kada kisa shi a ranki."

Cikin kuka tace
"Ya khaleel ka fada min Yaya za'ayi bazan saka shi a Raina ba? Pls tell me, kodan ba kai aka budi baki aka ce maka shege ba, kasan yanda nake ji a Raina kuwa?
Ita fa a nufin ta bani da uba, ta fada da bakin ta Kuma Kai ma kaji da kunnen ka tace wai a yawon duniya aka same ni, ko Dan an haife ni ina wata bakwai?
Yara nawa ake haifan su bakwaini Amma babu Wanda yake kiransu shegu sai ni, ko kuma Dan bani kama da mahaifi na ne?
Yara nawane ake haifan su Basu kama da mahaifin su Amma babu Wanda ya taba kiran su da shegu sai ni."

"Fannah relax, kiyi haquri Mana."

"Mtswwww, bani hanya na wuce"

Haɗe rai yayi ganin kaman lallaɓa tan da yake yi ne yasa take bauɗe masa, yace
"Babu inda zakije"

Ingije shi tayi ta fice tana Jan akwatin ta takai dai_dai kofar fita ya riqe ta.
"Nace babu inda zakije ko?"

Harara ta wulla Masa tace
"Sai ka hana ni nagani"

Ta sake fisgewa tayi waje tana qwala ma drivern ta Kira,
ta kusan ƙarasawa jikin motan ya ƙaraso da gudu ya dauke ta cakat yayi ciki da ita,
Ta dunqule hannun ta tana Kai mishi duka tana ihu da cizonsa a kunne Amma bai sauqe ta ba,
Sai da ya kaita dakin shi kafin yadire ta ya fito ya jawo qofa ya rufe.

Kuka take yi sosai tana buga ƙofa Amman yaqi budewa daga qarshe yaji kukan ta na neman karya Masa zuciya sai ya fita daga gidan gaba daya.

10:14am
Ya dawo cikin dakin ya same ta tayi shame_shame a tsakiyan dakin har ta chanxa kamanni,
Motsin shi data ji yasa tasan ya shigo Bata kalli wurin da take tsaye ba tace
"Cherry basai ka min wannan hukuncin ba nasan yanzu na zama damuwa cikin rayuwar ka Amman komai ya kusa qarewa."

HAR ABADA (Under Edition)Where stories live. Discover now