chapter 36

304 40 3
                                    

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

*🌹HAR ABADA🌹*
*(bazamu rabeba)*

*LOVE &* *FRIENDSHIP*

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/


Vote me on Wattpad @ayeeshatmuhd

RUBUTAWA

UMMU NAJMA

DEDICATED TO
MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA

Sis pha'ixer 🤩
Namesy💞
Sis adama💗
Ummu al'amin💘
Miss danzango❣️

Wannan shafin naku ne I LOVE YOU SO MUCH💌

36🍎

Cike da murna ta rungume mom tace
"Ameeen momy nah" sai Kuma tayi saurin janye jikin ta, ta rufe idon ta da hannuwan tana jin kunya.

Zungurin ta mom tayi tace
"Ai kin Gama zubar da kunyan,
tunda kin Sami abinda kike so sai ki tashi mu koma parlor Dan nasan lokacin barcin ki Bai yiba"

**********
2 weeks later

Tana zaune a parlor tare da Ayrah suna taba Hira, don dama Ayrah Bata da wani zafi, da ta samu Feenan ma Mai sauqin Kai ne sai ta sake da ita, sun dawo kaman qawaye duk da tana jin kishin ta a cikin ranta Amman ta sadaqar don ta fiskan ci zahirin soyayyar dake tsakanin su Wanda su sun dauke shi a matsayin sabo ne kawai.

Shigowa yayi fuskar shi dauke da murmushi Yana kallon Feenah, ita ma da sauri ta tashi ta nufi wurin da yake tsaye tana mishi sannu da dawowa, tunda suka dawo daga office yaci lunch ya fita Bai sake dawowa ba sai yanzu.

Kallon hannun shi dake boye a Bayan shi tayi tace
"Ya Ahmad Mai kake boye wa ne?" tare da Kai hannun ta tana qoqarin fito da abun da ya boye, da sauri ya matsa baya Yana girgiza Kai yace "guess".

Tabe baki tayi tace
"I can't guess anything kawai ka nuna mun"

" Ok ki rufe idon ki, Kuma idan Kika yi cheating bazan nuna Miki ba"

Rufe idon ta tayi tana Dan budewa kadan tana leqowa, yayi dariya hade da fadin
"Yarinya kenan, mani Zaki yi wayo? Ina ganin idon ki a bude fah, Ashe baki son kiga abin da na kawo Miki"

Da sauri ta rufe idon ta gamm tace" Aa ya Ahmad kayi haquri na rufe"

Saida ya tabbatar ta rufe sannan ya fito da wani takarda yace " oya open your eyes" a hankali ta bude idon ta ya sauqa Kan UNIVERSITY OF ILLINOIS CHICAGO (UIC) rubuce a saman takardan, Bata Gama mamaki ba taji shi Yana fadin.

"I've got u an admission wifey, jibi Zaki fara zuwa makaranta insha Allah"

Ihu Feenah ta sake cikin tsananin farin ciki ta dale jikin Ahmad tana Kai Masa kisses a cheeks dinsa, gogan naku Kam signal ne ya dauke Masa cakk, Ayrah na ganin haka ta tattara tsintsiyar qafafuwan ta tayi bedroom dinta qolla na cika a idon ta.

Murna sosai Feenah tayi ta sake shi tana Masa godiya bakin ta har kunne, shi idan za'a saka Masa wuqa kwata_kwata baisan me take fada ba, ya tsaya ne qeqam kaman gunki.

Tana Gama Masa godiya ta wuce dakin ta da gudu ta dauki waya ta Kira Ammi, (mutum daya a duniya da bazata taba baqin ciki ko hassada da ci gaban 'yarta ba *mahaifiya*💖) tana picking ta zayyane Mata alkhairin da Ahmad ya Mata, Ammi ba qaramin farin ciki tayi ba tana dada gode ma Allah da yaba ma 'yarta farin ciki da kwanciyar hankali, kafin ta katse wayan sai da Ammi ta shelanta ma duk yayu da qannen Feenah abin da yake faruwa, sosai suka Taya ta murna kowa ya karbi wayan ya Mata Allah Sanya alkhairi kafin ta musu sallama ta kashe wayan.

HAR ABADA (Under Edition)Donde viven las historias. Descúbrelo ahora