chapter 12

279 34 2
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

      🌹HAR ABADA🌹
          (bazamu rabeba)

       LOVE & FRIENDSHIP

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.com/pro__writers?s=09
  
         RUBUTAWA

        UMMU NAJMA
   
DEDICATED TO
MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA

12🍎

Sauqowa yake yi a hankali cike da izza wannan karon da dark designer shades manne a idanun shi.

Shaqar iskan garin yayi Mai cike da ni'ima ya sake wata kasalallen murmushi.

Gida ya wuce yayi wanka ya kwanta ya huta kafin ya fito ya dauro alwalan la'asar ya wuce masallaci yayi sallah.

Yana matuqar Jin Dadi idan yabar Abuja saboda duk wani takunkumi da wasu security suna raguwa,
Yau kanma ya yanke shawaran yawo shi kadai ne yaji dadin freedom kamar yanda kowa ni Dan Adam yake ji.

Shiryawa yayi cikin Balenciaga wears ya fito ya samu har Isa driver yayi warming maroon Nissan Altima ga wasu black range Rovers guda biyu na escort din shi.

Karban key din motan yayi yace musu su zauna shi dai tafi shi kadai ya fada cikin motar Ya yi gaba.

Driving yake yi cike da qwarewa Yana Jin dadin Yanayin da yake ciki gaban sa da bayan sa fili yake gani saboda babu inuwar motocin da kullum suke zagaye dashi.

Direct gidan uncle Omar ya nufa saboda yaji dalilin Kiran gaggawan da yayi Masa.

Yana Isa babu Bata lokaci akayi Masa iso wurinshi.

Zama uncle Omar yayi Yana nazarin shi na wasu Yan mintuna kafin ya gyara zama yace

"Ahmad"

"Na'am uncle"

"Allah Dan sassaba maka, ba daka maida mu mutanen banza ba,
Tunda shi mahaifin naka shayin ka yake ji to ni bani tsoron ka.

Shekaru kusan biyu kenan muna bin ka kayi aure kaqi,
kafi so sai ka gama tsufa muna Kai sadakan ka masallaci saboda an rasa yarinyan da zata amince ta aure ka ko?"

Tun mahaifin naka na shiru har ya qare ya koka da irin halinka, kodai baka da lafiya ne?"

Qasa da Kai yayi
"Lafiya na qalau uncle."

"Au, iya shege ne yake damun ka?
To yanzu fada mun wace yarinya kake so ka aura."

Sosa qeyan shi yayi yace
"Babu"

"Ina kafuran can qasar da tace tana sonka? ka aure ta mana tunda ta riga ta fada ma mahaifin ka."

"Wa? Wai Ayrah kake nufi?"

"Oho koma waye nasan ka gane ta, itan nake nufi."

"Aa uncle gaskiya ni bani son ta."

"Tunda Haka kace ba sai anje da nisa ba ga Yar uwar ka batula ka aura."

Kaman an fada Masa wani mummunan labari ya ware Ido tare da ja baya yace
"Batula!!! Nayi me da ita? Wannan baqauyiyar, a qauyen tsamiyan mahaukata take fa."

HAR ABADA (Under Edition)Where stories live. Discover now