chapter 59

357 38 0
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

      *🌹HAR ABADA🌹*
          *(bazamu rabeba)*

       *LOVE &* *FRIENDSHIP*

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09

  
Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

         *RUBUTAWA*

        *UMMU NAJMA*
   
*DEDICATED TO*
*MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA*

Wannan shafin naki ne ke kadai *nusee Yar amana* Allah yabar qauna 😍

59🍎

Yana kashe wayan Feenah ta saka kuka cikin ranta tana qara tsinewa Amrah albarka, Abdallah ma da ba wayo gareshi ba Yana ganin mahaifiyar shi na kuka shima ya ajiye fork din hannun shi Yana Taya ta.

Sauqa yayi daga kujeran da yake ya qaraso kusa da ita Yana Jan kayan ta, ta durqusa ta dauke shi, Yana share Mata hawaye shima Yana kuka yace
"Ctop ciyayin Ummi abbah bayi co"

Share hawayen ta tayi ta dauke shi, suka shiga daki ta tattari takardun ta kaman yanda Ahmad ya umarce ta, ta saka ma Abdallah kayan sanyi ta hada musu Kaya kadan sannan suka fita daga gidan.

**********

Motocin su na tsayuwa ya fita da gudu har Yana tuntube, Yana shiga ya Sami mom zaune da Sahar har yanzu Bata Dena kuka ba, Yana qarasawa gaban mom ya zuba Akan guiwowin shi ya hade hannuwan shi cikin roqo yace
"Dan girman Allah, badan hali na ba ki yafe ni, bansan mai aka ce miki har ya saka ki fushi Haka ba, bansan Mai yasa ake son shiga tsakanin mu ba, amman kisani ke kadai nake dashi a duniyar nan wanda zan Kira da sunar mahaifiya ta, idan Kika guje ni bansan Ina dan saka kaina ba, I'm still your son your beloved Ahmad, mom ko kin mantani ne? Ko yaushe kina fadamin irin son da kike min where is that love now? Ur my best friend my mentor my strength and my biggest weakness ana azabtar Dani ta hanyar ki mom, I'm not myself I'm no longer Ahmad L na koma want Abu daban Dan Allah ki taimaki rayuwa ta ki janye Allah ya Isan da Kika mun, zanbi ko wani umarni naki nayi alqawari"

Can qasan zuciyar mom tanajin qauna da Kuma tausayin Ahmad sai kuma wani abu daga can daban ya taso ya danneshi.

Ta qanqace idanun ta cikin masifa tace
"Ina Nafeesah?"

Shiru yayi Bai amsa ta ba don baisan mezai ce mata ba,
Tace "son dakai nace magana, me Nafeesah takeyi a cikin gidan ka? Me yakaita America? Kuma Mai kuke yi a tare ka bani amsar wannan tambayoyin sai nasan ko dagaske kake kana neman zaman lafiya da kwanciyar hankali"

Bayida zabin da yawuce yayi qarya ma mom dan harda rayuwan danshi a cikin garari idan tasan gaskiyar abinda ke faruwa.

Sauqe ajiyar zuciya yayi yace
" Feenah ta fara karatu Tun kafin mu rabu, shiyasa na taimaka Mata ta qarasa tunda ita uwar dana ce"

"Oho kaikuma gaka sarkin taimako ko? Ana taba ka saikace uwar danka To yau zanga ta iyawar ka, inason yanzu yanzu ka dakko takardun duk wani Abu da ka mallaka da takardun mu dake wurin lawyern ka kafin ayi sallar isha ka kawo min su, Kuma daga yanzu zaka koma qarqashin kulawa ta kaman yanda ka fada Ina maka a baya, ko wani motsi naka zan Sanya Ido akai kada ka taba tunanin yaudara ta don tunda naqi Nafeesah na koreta daga familyn nan ta koru Kenan babu Wanda ya Isa ya dawo min da ita ka tafi yanzu ka dauko min takardun companies dinmu na bawa Amrah ajiyar su tunda Kai bazaka iya kula dasu ba nasan ita zatayi"

HAR ABADA (Under Edition)Donde viven las historias. Descúbrelo ahora