chapter 65

440 40 0
                                    

(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)

      *🌹HAR ABADA🌹*
          *(bazamu rabeba)*

       *LOVE &* *FRIENDSHIP*

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

INSTAGRAM: https://www.instagram.com/proficient_writers/

FACEBOOK: https://mobile.facebook.com'/groups/2455147078097572/

TWITTER: https://twitter.come m/pro__writers?s=09

  
Follow me on Wattpad @ayeeshatmuhd

         *RUBUTAWA*

        *UMMU NAJMA*
   
*DEDICATED TO*
*MAMAN MAMY SHALELE AND BEELAT SARAUNIYA*

65🍎

Fitowa sukayi daga part dinsu Yana gaba tana biye dashi a baya, ta marairaice fuska tana faman roqon shi amman yaqi kulata, riqo hannun shi tayi ya juyo Yana kallon ta tace
"Please hayaty just once ka bani goyon baya nayi wani abu Mai kyau please, idanma baka yarda da abin da na fada maka bane kasa a sake bincika maka Majeed ciki da waje , kodan future na wa'innan yaran da take dashi, Yaya Imran ya rasu Amman yabar baya ka taimakeni wayan ganin rayuwar bayan da ya Bari ya inganta"

Sauqe numfashi yayi yace
" Na yarda Majeed mutumin kirki ne komai na rayuwan shi Wanda za'a iya Ido take gani NASA an samo min Amman ita Aishan tana sonshi ne? Ko Kuma qoqari ne kawai irin naki Zaki hadata Dole da Wanda Bata so".

" Ai shiyasa nace ka taimake nin in samu nayi magana da Majeed din lamarin Eesher Mai sauqi ne nasan abinda zanyi a kanta"

" To sai ki Bari idan na tashi a aiki sai mu tafi tare Kinga yara zasuyi lattin makaranta ni zan wuce" ya fada Yana tafiya.

Sake riqo hannun shi tayi tace
"Aa hayaty ka bari idan naje ni kadai maganar mintuna kadan zanuyi na dawo gida"

Ya zabga Mata harara yace
" Amman Baki da hankali, dake ni sakarai ne sai na barki kinje can wani uwa duniya ki gana da wani qato? To ban amince ba idan ba Zaki iya haquri na dawo ba saidai a bar maganar kawai"

Sassauta murya tayi take" Aa kayi haquri, sai ka dawo din Allah ya kiyaye hanya"

" Ameeen" yace ya tattari yaran suka shiga mota suka wuce.

Tun Yana office ya tura ma Majeed invitation Yana son ganin shi da yamma a L mansion.

Bayan yazo sunyi Yan gaishe gaishe ne Ahmad ya fara magana
"Na gode da ka amsa gayyata ta Amman wannan zuwan ba nawa bane, hearty ce ke neman kuyi wani magana Mai muhimmanci, Amman dan Allah inaso ka fahimce mu cikin al'amarin Nan babu Dole, idan har baka so you are free to refuse dan sasantawa muke nema saboda dawo da farin cikin da ya gushe"

Gaba daya maganar Ahmad ya daure Masa Kai ya rasa Gane inda ya dosa, Feenah Kuma ta zuba Masa Ido tana son ya tashi ya Basu wuri su zanta Amman sai qara gyara zama yayi ya Ciro wayarsa Yana dannawa.

Ganin haka yasa kawai ta fara magana
"Yaya Majeed" ta Kira sunan shi a hankali.

Dagowa yayi ya zuba Mata idanuwan sa masu rauni take
" Ka tuna lokacin da muke model?"

Murmushi yayi yace "yess of course" Yana tuno irin rayuwar da yayi a baya.

"Su waye qawayen ka?"

Nan ma murmushi yayi yace
" Feenah da Eesher"

"Cikin su wa tafi sabawa dakai?"
" Aisha"

"wa tafi ta taimakon ka da baka kulawa sannan was tafi fahimtar ka?"
" Aisha"

HAR ABADA (Under Edition)Tahanan ng mga kuwento. Tumuklas ngayon