chapter 9

479 45 4
                                    

#Duk asanadin soyaya #

💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦BY💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦 SAFNAH 💦💦💦💦💦
💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦ALIYU
💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦
💦💦💦JAWABI
💦💦💦💦💦💦💦💦💦💦

Bismillahi rahamanin rahim

Cikin fusata yace, "raihan kasan abinda Kake faďa kuwa? Kasan wacce Kake lakawa wannan mummunar kazafin kuwa?

Rausayar da kansa raihan yayi yace, "wallahi ALLAH abba babu ďigon karya ko kazafi acikin magana ta, idan kuma baka yarda ba,nina yarda kazo muje gunta da daddare zaka same ta dawani, abba harfa cikin gida take shigar dashi.

,"shikenan ALLAH yakaimu daran ina jiran ka kazo ka kaini inganewa idona ,tashi yayi ya shige ciki yana nazarin maganar da raihan ya faďa masa kan AISHA labiba.

Safa da marwa raihan yashigayi dan samawa kansa mafita, murmushi yayi ya ciro wayar sa ,yakira kiran Sadiq yayi, cikin ikon ALLAH kuwa ringing ďaya Sadiq ya ďauka, hakuri sosai raihan yayita bawa Sadiq kafin ya sauko Dan sosai ya nuna masa bacin ransa,rasayar da murya raihan yayi yace, "Yauwa kasan abinda nake so kayi min?

Girgiza Kai Sadiq yayi kamar raihan din yana ganin sa yace, "saika faďa "

Rausayar da murya raihan yayi yace, "Dan ALLAH sonake ka taimaka ka taho anguwar mu anjima da daddare, sonake karakani gun labiba na bata hakuri.

"lalai saida Nina zaka tafi bata hakuri?

"kayi hakuri aminina kasan halin Inna ta yanda take,bata son taga ko hanya ta haďamu da labiba, bare ace zancan Aure, yanzu ma abba nane zai tsaya min, amma da sharaďin babu Wanda zaisan Nida ita muna tare Dan yanzu ma cewa yayi saidai murinka Hira acikin gidan su.

,"Cikin gida fa kace ?

,"Eh Dan hakanne kawai mafita,yanzu ma zaka rigani zuwa domin zuwan nawa saida taku idan zaka taho ka kira ni.

,"Shikenan kawai sadiq yace sannan ya ije wayar.

Ana idar da sallar isha'i kuwa Sadiq ya kira raihan ya shaida masa zuwan nasa.

Cikin sauri raihan ya isa gida, kiran abban sa yayi yace,"abba kayi sauri Dan yanzu naga wucewar saurayin nata .

Cikin sauri suka nufi gidan su labiba, labewa raihan da abban sa sukayi, suna kallo Sadiq ya faka motar sa, Jim kaďan saiga labiba ta fito dake yariga daya shaida mata zuwan nashi ,lokacin da sadiq ya shaida mata abinda raihan yace, "jiransa acikin gida da kuma inda zasu rinka yin Hira sosai Abin yabata mamaki, amma sanin Hali irinna Sadiq yasa ta amince suka shiga cikin gidan.

Nunawa abban sa labiba da Sadiq yayi lokacin da suka shige cikin gidan, rike haba malam sule yayi yace ,"lallai yaran yanzu saidai abarsu, shiyasa akace ba'a shaida ďan yau.

Murmushin samun nasara raihan yayi sannan suka nufi gida.

Suna isa gida raihan yakira Sadiq ya zura masa uban karya, da cewa abba bashida lafiya, hakuri yabaiwa labiba sannan ya shaida mata rashin lafiyar malam sule.

DUK A SANADIN SOYAYAWhere stories live. Discover now