61/62

621 22 0
                                    

❤❤💋💋
IHSAN
❤❤💋💋

(Romantic, Love, Sorrow)
❤❤💋💋✨✨🌟🌟

Written By
Khadeejaht Hydar.✍🏻
Young Novelist🧕.

💫🌟FAGEN MARUBUTA WRITERS ASSOCIATION🌟💫

❤🌟Gidan zaman lafiya,Hadin_kai da yardar juna Insha Allah❤🌟.

Dedicated to
Bloddline Aliyu Hydar.

    
     ✨🌟61/62🌟✨
Farha tace"...Ni jikina na bani zamu samu labarinta nan kusa,Amma Allah yasa inmunsamu kar Inna taji."

Mama tace"..Ai ko munganta bazamu sanar da'itaba,Mamansu Farha tace"...uhm ai yanzu abun duniyama ya isheta  tunda aminiyarta ta da d'anta sun juya mata baya."

🌟🌟✨✨✨❤❤❤
Yana zuwa ya taradda su Fahad na jiransa yace"... Am sorry for coming late, Hisham yace"... Is OK."

Bayan sun gaisa sun kuma bude taro da addu'a saboda wannan tazama d'abi'arsu inzasuyi komai sai sunyi addu'a,soboda dukansu akwai ilimi sai isa iyayennasu basuda shakka akansu.

Bayan sungama addu'a ne suka d'an sha juice mai sanyi sannna Fahad yace" Deen jiyafa Baba ya sameni a gida yace"Nan da wata 🖕inkawo masa wacce nakeso inba hakaba a wata dayan zaibani wacce yaga dama,yace".... Bani kadaiba harda Ku wai sungama magana dasu Baba ma."

Ajiyar zuciya Hisham yayi yace"....Ai Babu matsala tunda kowa yanada wacce takeso,Deen yace" yauwa wai ya maganar zuwa kauye anjuma ne?Fahad yace"..to sarkin rainin hankali ana wata magana yana kawo wata."

Deen yace"....To naga angama  maganar aii kawai ayi auren nan da sati  ✌😜,Fahad yakaimasa duka yace".... kaji  Mara kunya."

To aiba rashin kunya bane cewar Hisham, tunda dukanku kun nuna kuna son auren ai sai isa su Baba suka matsa muku don karku lalace.🙈🙈

Deen ne ya tashi yana dariya yace"...to ai gwara mu munnuna munaso,wasu da suka b'oye mukasan abinda suke k'ullawa."

Fahad yace" wallahi Kuwa,Hisham yace" ...ai zamuji bayani  nan gaba."

Deen yace"....nide Ku tashi muje mu shirya kawai mu hadu a hanya indaukeku,zanje na shirya  in dauko su Baby."

Ohk ba damuwa cewarsu Hisham,sannan kowa ya kama hanyar gida don shiryawa.

Yana parking d'in motarsa bangarensu Habibty ya nufa,Ummi da Su Angel ya tarar a parlour   ya gaidasu sannan yace".... Angel   ba'a fad'amiki  ki shirya zamu fita ba?"

Tace"... A'a ba'a fad'a minba amma bro where are we going?,mama tace"..kije ki fad'awa daughter ta shirya yanzu Ku fito,tace" ..to tawuce don cika umarnin Mama."

Mama tace"....Bance maka Ku  dad'e ba fa ,kuma dafatan kayimusu tsaraba?,yace" ...eh mama na musu kuma insha Allah bazamu dadeba tace"...Allah ya muku albarka yace"... Amin."

Tana kwance Angel taje ta sameta tace"... Sis mama tace"...Ki tashi Mi shirya zamu fita,Jin an ambaci mama ne yasata tashi ta shirya cikin doguwar riga baka mai matuk'ar kyau. "

Ko kwalliya batayiba illa kwalli datasaka sai dan kunne farare k'anana,sai ta saka hijab d'inta white karami saboda ita tagwammaci tasaka karamin Hijab akan gyale.

Masha Allah nace"..Ganin kyawun datayi, Angel ta kalleta tace"...Masha Allah Matar bro kinyi kyau sosai wlhh,Ihsan tace"....to Mrs talkative(mai surutu) zo mu tafi tace"... toh muje."

Saukowa sukayi dai_dai lokacin Deen ya fito cikin shigarshi ta white nd black,Tsayawa yayi cak ganin yadda ta koma kamar wata balarabiya ga oily brown eyes dinta me matukar daukarmasa da hankali yakara kyau.

Ganin yak'i daina kallonta ne ga mama na zaune ne yasakata d'auke kanta,taje gaban mama ta tsugunna tace"... Mama munshirya,Mama tace"... Masha Allah Kinyi kyau y'ata murmushi tayi ta sadda kanta kasa."

Mama a zuciyarta tace"... Yarinyarnan bade kunya ba ,kuma kunyarta na burgeni."

Mama tace"... Ku tashi Ku tafi karkuyi dare ku gaida su gaba d'aya,To ta amsa dukda batasan gunsuwa zasujeba."

Suna fita Ya d'akko sabuwar motarsa kirar Benz a parking lot,Baya ta shige Angel ma haka,Juyowa yayi yace"... Uhm Baby na kidawo gaba yazakumin wayo ku tare a baya kubarni nikadai.

Angel tace"... sis ki koma gaba,tace" ...A'a ke ki koma nafison zaman baya."

Tace"...kinga su yaya fahad anjuma zasuyi joining d'inmu plss kije takarasa da fuskar tausayi,batayi magana ba ta fito ta zauna a gaba ya tada motar suka bar gidan. "

A hanya Angel tace" Bro ina zamuje yace"....Gurun kishiyar sis d'inki,jin haka ne yasa Ihsan k'ara daure fuska ta maida kallonta ga titi.

Angel zatayi magana Taga su fahad ,tsayawa  yayi ya daukesu suka ci gaba da tafiya.

Tana zaune tayi bacci a cikin motar,uhm nide nace baccin kishi ba lol😜.

Suna isa Angel tace"... wow bro daman nan zamuzo shine kake tsokanar sis,suna isa Hisham yace" ... Ki shiga kimana sallama "

Tana shiga su Farha na zaune suna ganinta suka tashi suna murna ,Meesha tace"...Bismillah ki zauna tace" Tare muke da yaya Hisham da Fahad."

Mama tace" ki ce musu au shigo ai nanma gidane,fitowa tayi tace" yaya Ku shigo binta sukayi banda Deen dakeson ya tashi Ihsan."

Cikin barci taji ana   tab'a mata fuska da sauri ta tashi,amma ganinsa yasa ta kauda kanta gefe.

Saurin juyowa tayi ganin kofar gidansu meesha take,kofar tayi niyar budewa amma ya rikemata hannu yace".. aikina fushi dani bazaki shigaba ,komawa zamuyi."

Da shagwaba ta juyo tace"... ainadaina fushin plss ka budemin  shiga, murmushi yayi yace"....to muje."

Meesha ta kalli Angel tace"...kunji me....bata karasaba Ihsna tayi sallama tashigo."

Vote
Like
Share
Comment

IHSANWhere stories live. Discover now