My Nikkab

1.9K 157 42
                                    

https://my.w.tt/xtVVXjuXhcb
MAH~NOOR✧✧
   My First Wife♡
        Chapter 1️⃣5️⃣
     MrsUsman400
Free book 🤩
For You Jikar kulu

BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM

Zee Sardaunan
Sumayya Ahmad Aliyu, fateema Mustapha
Ga gaisuwar ku nan🤩😘 masu jiran Mah-Noor.....

_🤣Gaye You enter Noorh hand, zaka fadi gaskiyar ka, indai Noorh ce jininka sai ya kare, Yan leken asiri, naga sakonku! Wattpad fans kuma haka, My Hajiya Maryam Jikar kulu 🤣 Mommy Sultan kece kike bayan Noorh kowa ya fara jin haushinta_

#My Nikkab
Yana cikin gym room, yana d'aga karfe. Sako suka fara shigo mishi. Cikin gajiya da karar wayar shi, ya d'auka yana kallon Ummina, kiranta na katsewa hadiya tana kiran shi, dauka yayi tare da cewa.
"Beb!"
"Ka duba tweeter please!"
Cikin sanyin jiki ya bude idanun shi, sanan ya bi wayar da ta kashe da idanu, kafin ya tashi zaune yana jin faduwar gaba, a hankali ya bude data. Sannan ya shiga tweeter. Sako ne suka shiga sauko mishi, cikin faduwar gaba yaga sakon Noorh. Ji yayi zuciyar shi kamar zata diro kasa, ya kurawa yar ido.

           Lokacin guda yaga Aysar Haladu, wani matashin me kudi anan Yola, yana mara mata baya cikin tsannanin b'acin rai ya shiga hango wasu daga cikin mutanen da suke gaisawa sama sama, kira wayar shi akayi cikin mugun zuciya ya dauka.
       
"Lion! Gobara ta tashi a cikin kamfanin amma anyi nasarar kashewa."

     Sake wayar yayi tare da dafe kirjin shi da yake barazanar fashewa. Jingina yayi karfen da ya d'aga, ta sauke a kansa ba dan ya tare ba, da wallahi tayi mishi lahani. Ji yayi zuciyarshi tana ci da wuta. Dan haka ya mike tare da tangadi ya bude yar medium din frig din da yake gurin ya bude tare da daukar goran ruwan sanyi ya bude bakin shi sai da ya shanye tass. Yayi wurgi da goran yana sauke wani irin gurnani.
       Da zai sami wani a kusa dashi tabbas sai yayi mishi mugun duka, tashi yayi zuwa dakin shi ya budewa kan shi ruwa, haka ya jike jagwab. Sannan ya nufi inda towel ɗin shi yake ya dauka tare da daurawa yana goge kanshi da da daya.
         Wani irin huci yake, tabbas da zai ga marubucin wancan abun sai na lahira yafi shi jin dadi, wani irin bakin ciki yake ji kamar zai kone, haka yayi ta ambaton Allah.

    Har ya gama shiryawa sannan ya fito, yana fitowa yaga Nazzir ya wani firgice, bai ce kome ba, ya shiga mota aka tafi da su kamfanin, kafin su iso an kwashe kome. Sai an kananun kayan da aka barshi suna cikin wuta, lumshe idanun shi yayi domin ji yayi kamar zai sake kuka, Kamfanin nan amanar shi ce.

         Mahaifin shi ya bar mishi, duk da yana da wasu masana'antu amma wannan ji yaƙe kamar mahaifinsa ne a raye.

"Kuyi hacking din Acct ɗin Tweeter din marubucin, duk wanda yayi rubutun nan makusancin kamfanina ne, ku tafi ki nimo min wanda yayi wannan ta'addanci..."
"Lion! Jornalist!"
Juyawa yayi da fuskar shi da tayi jajjur.
"I don't care! Koma waye yazo babu abinda ya dame ni, kuje ku nimo min wanda ya lalata min suna. Idan ba haka ba, toh wallahi zaku ji a jikin ku."

            Yaki magana da yan jaridu, asalima abin sai ya koma siyasa, domin wasu na cewa sharri aka mishi wasu na kuma cewa zai aikata idan aka yi dubi da yadda yake da Arziki gashi matashi wanda yake ganiyyar samartaka shi. Dole yayi abinda ya gadama.
  Yana zaune a kamfanin anan yayi Sallah magarib da isha, suna zaune ana cigaba da aikin, aka turo Super visions from ministry of health, da Kuma wasu daga Shari'a committee, tare da Da'awa. Mahir ya kasa magana, a hankali aka shiga bincike sosai, binciken da ya kai har sai da aka zakulo wasu abubuwan na daban, ba abinda ake zargin ba.

              Dake duk abinda yake faruwa ana dauka a live, karfe goma na dare Ummi da wasu manyan lauyoyyin daga lagos suka iso. Anan aka shiga tashin hankali tare da musayan kalamai.

MAH~NOOR🌹Onde as histórias ganham vida. Descobre agora