💖💫RUDANI💖💫 51

101 26 43
                                    


Ya koma daki amma ya kasa komai, tunani kam Ilhaam tasa sa cikin sa, after much of it ya yanke shawara, shirin bacci yayi ya koma dakin nata, tana kam shirin bacci ya sameta "I am sorry, I shouldn't have reacted the way I did earlier" ta bada haquri bayan ta karaso wajen sa "I trust you Anwaar, you are my husband anyway, forgive me please" tayi saurin rike hanun sa "You don't have to" ya dagata ganin ta durgusa "We are in this together and we will In Shaa Allah find the best solution" ya kwantar mata da hankali "I love you Anwaar, please don't leave me" she tried kissing him as he leaned ganin tsayin ta bai kai ba "Wait, you are on your period right?" Girgiza kai tayi ah hankali "I felt like drinking that smoothie fa" ta mishi bayani gane dalilin sa na fadan hakan, bai sake ce komai ba ya dauketa ya sata a kan gado........ Washegari da wuri Teemerh ta tashi har mamaki abun yaba Anwaar dan yasan tashi da wuri ba nata bane, gaisuwan mutunci tayi da Ilhaam dan tasan kwanakin Ilhaam sun kare a gidan, ita tayi breakfast ta shirya komai yanda ya kamata, gidan ne kadai bata gyara ba dan jira take baiwar ta Ilhaam ta gyara sa, dakin Anwaar ta wuce ta samu yana shiryawa, ta fasan Ilhaam suppose to do the necessary things amma dan neman magana taje wajen nasa, dan siririn tsaki taja hango tattoo nasa sannan ta karasa "Mr. Right naji kaman ance tattoo haramun ne" ta fada da sigan munafurci yanda bazai fahimci haushi takeji ba dan kullum ta gani sai ranta ya baci "Kaman?" Ya tambaya dan tabbatar da abunda ta fada "Eh, am not sure" ta fada tana duba masa kayan dazai sa, bai ce mata komai ba dan gani yake ae she's helping Ilhaam "So baki ma sani ba? Fatima kinyi attending Islamic school kuwa?" Ya tambaya da mamaki saboda ya kasa gane mey ya aura, he wants someone religious "Toh ae karya ba kyau, nayi attending Islamic school, of course, amma ban gama ba" ta fada sannan ta ajiye masa kayan nasa "So you knw none of the Hadiths and other Islamic books apart from the Holy Qur'an?" Tace "Toh ae shima ban gama sa duka ba, nayi yakai rabi hala, kawae naga ban iya sauran" ta fada irin koh ah jikin tan nan "YaMujeeb" ya fada yana kad'a kai dan yanzu yasan dalilin da yasa Fatima keyin wani shirmen, tanada karancin ilimin addini "Babe, yanzu dai ba wannan ba, breakfast is ready, and you will like every of it" ta fada sannan tayi dagel tayi masa peck a cheek ta fice dan baso takeyi suja tadin ba tunda taga ya fara mata tambayoyi, kallonta yayi har ta fita dan ya rasa mey ke damun Fatima yau, in bai manta ba Ilhaam will be the one to cook, barin tunanin yayi dan su ba'a gane musu, Ilhaam kuwa harta gyara gidan tasa turaren wuta koh wani angle cikin electric incense burner, saukowa Teemerh tayi ta sameta tana gyara incense waterfall, tabe baki tayi ta karasa "Erm..Ilhaam aiki kike tayi ashe" ta fada ba yabo ba fallasa, dagowa Ilhaam tayi ta kalleta batace komai ba "Sai kiji mutum ki wani yi banza dashi" Teemerh ta fada sannan ta karasa dining area dai-dai da fitowan Anwaar, lumshe ido yayi jin kamshin sannan ya bude su a hankali, shifa in yaji kamshi kawae yanajin farin ciki "Ina kwana" ta gaishe sa cikin nutsuwa "Im fine Angelic, let's eat" ya fada sannan ya kama hanunta suka karasa, kujera taja ta zauna ba tare da tace ma Teemerh komai ba, Teemerh ce ta tashi tayi serving Anwaar, zatayi serving Ilhaam, Ilhaam tace ta bari zatayi da kanta "Ke meyasa ba'a miki gwaninta ne?" Anwaar ya tambaya Ilhaam ganin ta dakatar da Teemerh "No bawae baa mun gwaninta bane ba, I can do it myself" baice komai ba ya fara cin cinnamon rolls "Sai kiyi tayi ae" Teemerh ta fada ciki ciki, amma saidai Ilhaam tajita, kallonta tayi rai bace sannan ta serving kanta, tasan Anwaar ya fara biyewa Teemerh sarai amma ba yanda ta iya sai haquri, ba laifi girkin Teemerh yau yayi dadi dan ta basa mahimmanci "Babe, amma zaka saukeni ah gida koh?" Kallonta yayi kaman bazaiyi magana ba, sai chan yace "Afternoon flight zaku bi right?" Tace "Yeah, why?" Yace "Sai ki bari anjima kije gidan naku" taji haushi fa, amma ganin Ilhaam wajen ta danne "Shikenan Mr. Right, duk yanda kace haka za'ayi" ta fada da murmushin dole, yana gama ci ya musu sallama ya fita, Teemerh dake ita batajin magana tana ganin ya fita ta shirya tsaf itama ta fice abunta hankali kwance, gida ta nufa yanda ta samu su Mum har sun shirya tsaf ita suke jira "Ke lafiya sai yanzu kike zuwa?" Aunty Sham ta fada tana wani bata fuska kaman an mata wani abu "Anwaar bai fita ba sai yanzu, kuma yana fita na fito" Xeee ne ta kalle su batace komai ba "Amma dama tafiyan bada rana bane?" Teemerh ta sake tambaya "Toh ae koh da rana ne ke da wuri ya dace kizo ah shirya" Mum dake zaune kusa da Xee ta bata amsa "Ya ita aljanan take?" Shamsiyya ta tambaya, gane Ilhaam take nufi Teemerh ta tabe baki "Tana gida ba" ta fada tana hura hanci "Kina shirun ki 'yar albarka yau sai ta bar gidan Anwaar, naga kudin da kika turo, ya isa ayi komai ah gama lokaci guda" Mum ta fada da murmushi, ganin yanayin Mummy yasa Teemerh murmushi itama tasan tayi abun arziki "Sannu Yaa Xee" ta fada ganin bata kula taba" Xee tace "Sannu" kaman batasan magana "Wani abu ya faru ne?" Teemerh ta tambaya ganin amsan data bata "Kinaga dan iskan yaron chan Mahmoud ashe jinya ya tafi yiwa wancan buzuwan saboda yaji ciwo bana kare ba" Mummy ta fada tana ciza baki cike da takaici "Ae Yaya munyi ragwan azanci da bamu cire masa santa cikin zuciyan ba, amma yanzu za'ayi mey gabadaya, Xee dai bazata koma masa ba sai yazo dan mu bin mu ake badai mubi wani ba, ae duk taurin kan nasa da bai kai mijin Fatima ba, gashi ya fara biyuwa bare wani Mahmoud chan banza" Sham ta fada tana kwantar wa Xee da hankali ah haka "Toh wai ni auren ma dole ne? Ga masu kudi koh ina ah fadin kasan nan kuma nasan Zainab tawa mey kyau ce ba wanda bazai sota ba, sai ya sauwake mata ta dawo mu zauna, gashi ranan chan Alhaji ya ganta mu kace tazo yinin gida ne, yanzu ya sake ganinta nan kusa ae yayita bala'i kenan tunda yasan halin mijinta na hana fita" kallonta Xee tayi jin abunda tace, tasan yanzu ya kama Mum ta saida su ma tsaf zatayi hakan, banda haka kudin Mahmoud bey mata ba toh wani irin kudi takeso, kaman zata fashe da kuka kuma ta daure "Mum kinsan Mahmoud na sona, dangin sane suka dage sai ya kara aure wai ya samu magaji ba yin kansa bane" ta fada ah nitse "Toh ae kuwa shida dangin nasa garin nan ya kasa mana, ba wanda ya isa yaci mutuncin 'Yata, banda shegan taka yaga uwarki da kishiya koh qanwar uwarki da kishiya? Shamsiyya fada musu yanda kika ma kishiya, ah kwana biyu ta kori kishiyar ta kuma har yau mijinta bai sake tunanin aure ba, wai fa ah haka ita taje ta samu kishiyan, inaga in ita aka zo aka sama?" Mum ta fada tana huci, kallonta Teemerh tayi sannan ta daga ido ta kalli Aunty Sham ta tabe baki, dama itace ta kori Ilhaam mana, dan batayi zaton zata zauna tayi watanni da Ilhaam haka ba, amma duk da haka bai b'aci ba "Mum kun shirya komai?" Teemerh ta tambaya sannan ta tashi "Eh kije ki duba kiga abunda bayi ciki" Shamsiyya ta bata amsa, sama tayi nan suka cigaba da karantawa Xee darasin daya kamata ta sani

💖💫RUDANI💖💫Kde žijí příběhy. Začni objevovat