💖💫RUDANI💖💫 80

53 24 81
                                    


Watan su uku kenan da dawowa Abuja. Gidan Yaa Abu aka kaita amma taki zama dan bata fita, in zata fita kuwa saida wasu securities. Aameer ta kira ta dunga hada sa da Allah yazo ya dauketa ita bata iyawa dan kuwa ta kira Aameen yace ta haqura ta zauna she will be safe with Yaa Abu, amma ita bataji, dakyar shima Aameer yazo sukayi wasu maganganu da Yaa Abu before ya barsa ya dauki Ilhaam with some conditions. Nan fa Maāmaa tace Aameer ya kai mata Ilhaam, uwar mey zata zauna ta masa a gida ita ba matansa ba. Yaso yaqi amma ganin shi kansa Yaa Abun ma ta kirasa ta wanke sa tass yasa ya yarda ya kai Ilhaam "Maāmaa sure there will be lonely here, I agree that Yesmin is here for the meantime but she's married and can go back to her husband anytime, allow me to live with Aameer since Ash is there" Ilhaam tayi pleading "Nifa Ilhaam bazaki fahimci abunda nakeso ki fahimta ba" Maāmaa ta sake fada "Maāmaa please, zan yini anan yau, anjima sai ya dawo ya daukeni koh Aameer?" Ta tambaya tana kallonsa, shiru yayi jiran jin mey Maāmaa zatace "Ilhaam ya kamata ki fahimci bakomai kikeso zaki samu ba, bansan zaman ki wajen sa" Maāmaa ta dage kan abunda take fada, jin hakan Ilhaam tayi shiru "Toh ka dawo anjiman ka dauketa, sannan a kula" ta fada gane Ilhaam dai ta fison gidan chan, ba yanda ta iya ne tayi shiru, Aameer yace "Allah ya kaimu" sannan ya musu sallama ya tafi "Kin dai ci abinci ina? Ki bar zama da yunwa you know your condition" murmushi kadai Ilhaam ta mata, tashi Maāmaa tayi zuwa Kitchen Ilhaam na zaune wajen tana neman Yesmin kaman zata ganta "Gashi sha wannan, it's good for pregnancy" ta bata Coconut water, karba tayi sai a lokacin tace "Ina Yesmin?" Dan juyawa Maāmaa tayi dan har ta manta Yesmin na gidan yanda ta bata shiru "Ae batasan kinzo ba da kin ganta, tana chan wai en uwan mijinta na mata gyaran jiki, kinsan taki zaman auren ta dawo" saurin tashi Ilhaam tayi zuwa ganin ikon Allah "Zauna ki shanye tukun" ba musu ta zauna ta shanye da sauri ta tashi zuwa wajen Yesmin, tana ganinta ta tashi da sauri "Ilhaaaam" zatayi hugging nata Ilhaam ta matsa "Ni karki batan jiki" matsawa Yesmin tayi "Yawwa ga Ilhaam" ta kama hanunta kaman dole suka karasa, gaishe su Ilhaam tayi kafin Yesmin tace "Wannan Aunty Sofia, wancan Aunty Ruqs. Sisters din Rafeeq ne" ta fada tana murmushi kafin Ilhaam ta fauce hanunta ganin ta bata mata "They are lovely" Ilhaam ta fada kafin ta zauna kusa da su "Wannan itace mey yin gyaran jikin" ta nuna mata wata daga gefe "Aunty Soffy mey ma sunan gyaran?" Tace "Halawa" Yesmin tace "Yawaa Ilhaam sunan abun Halawa, it's waxing in English right? kizo a miki kema" juya mata fuska Ilhaam tayi dan ah duniya ta iya ma Yesmin halin banza "Ke kikaji wajen" Yesmin ta fada sannan ta koma ta zauna "Anjima mijina zai zo kinga sai ku gaisa ma kullum saina masa labarin ki" sake baki Ilhaam tayi tana kallon Yesmin, wai mutumin da kullum sukayi waya sai ance ba'so kenan, murmushi kadai sisters in Rafeeq keyi Yesmin na zuba musu labari, they love Rafeeq so much shiyasa da suka lura yanasan Yesmin itama suke santa, kuma koh dazu a gabansu da yazo ta dunga ce ae ya cuceta, ganin bai damu ba suma suka zubar da abun, labari iri da kala Yesmin tayi ta zuba musu har aka gama Ilhaam na zaune wajen tana kallon ta, Yesmin ta kara kyau sosai abunta "Yesmin zamu tafi, sai zuwa gobe kuma koh ita kadai zata zo" Aunty Ruqayyah ta amsa "Toh Allah ya kaimu" nan suka fita danyin sallama wa Maāmaa ita kuma taja hanun Ilhaam zuwa daki saboda labarai "My husband this my husband that. Haba Yesmin ki bari mu huta mana, tun zama na chan ba sunan wanda kike maimaita wa sai nashi, inda za'ayi magana kuma kice ba sanshi kike ba" tabe baki Yesmin tayi "Toh an dai riga an aura mun shi ya na iya?" Shiru Ilhaam tayi jin rainin wayon da Yesmin ke mata "Shi kuma wannan gyaran jikin ma wa kikeyi?" Tace "Ahh, shknnn ni bazanyi abu naga na kara kyau ba sai lalle in ma wani kato nayi?" Ilhaam tace "Munapuka, Allah ya shiryeki" dariya ta fara kafin taja Ilhaam zata mata gulma a kunne "Ke mu kadai ne fa dakin nan, say it out kawae" Ilhaam taqi bada kunne "Toh maganan gaskiya dai na fara san Rafeeq, kuma kullum sai yazo barin fada miki anjima ma zaizo, kuma Allah bazan kwana a gidan nan ba sai gobe da safe na dawo" sake baki Ilhaam tayi tana kallon hypocrisy "Ilhaam daina kallo na, ba mijina bane?" Tace "Mijin kine amma ki zauna ah gidan nasa mana, ban gane kullum kina nan kuma baki kwana anan ba? It's been 3 months Yesmin, ya kamata kibar komai ya wuce" Tabe baki ta sakeyi "Toh in na kwana anan mijina zai kwana anan ne?" Saurin girgiza kai Ilhaam tayi danta rasa abunyi kuma "Su Ilhaam ba'a iya soyyayyah ba" ta fara teasing Ilhaam "Barin ma kirasa nace ga matan Anwaar tazo, yazo ku gaisa, nifa har nace masa Anwaar ya sake ki, kinsan ae ba abunda zan boye masa mijina ne" sa hanu Ilhaam tayi akai ganin wannan yarinyan fa bata iya soyyayyah ba, tana farawa take haukacewa, shiru dai ta mata ganin ta fara wayan, harda basa time wae kar ya wuce, shima dake biye nata yakeyi yace ta kara 30mins kai dan yanzu yana aiki amma zai bari yazo "Gashi zuwa fa Ilhaam, wlh kikaje kika ba mijina attitudes zamuyi namu" Ilhaam tace "Toh mey? Ba gaishe sa kawae zanyi ba?" Tsaki Yesmin tayi kaman ta tuna wani abu tace "Anwaar na zuwa wajen naki kuwa? I want you guys together again" Tace "Yaje, kullum ma sai yaje amma bamuyi magana ba, haven't you told him I went to Maiduguri?" Yesmin tace "Eh", "Toh yaje ne? Ae bai damu dani ba" hararan Ilhaam tayi ganin ta iya fadan rashin gaskiya, itafa tace kar a fada masa saboda bataso yaje, yasani kuma tana blaming nasa baije ba "Barin yi wanka kafin Rafeeq yazo toh" tana fada ta tashi. Rafeeq yazo dan yakai wajen 20mins da zuwa ma Yesmin wae shiri takeyi ya jirata "Ilhaam muje toh" ta tashi bayan ta gama shirin, gyara mata veil in Ilhaam tayi kafin suka fita, yana zaune shi kadai yana kam danna waya, kamshin daya ji ne yasa ya dago ya kallesu "Kazo kenan" ta fada sannan ta zauna kusa dashi Ilhaam ta zauna different seater "How are you?" Ya dan sunkuyar dakai yana fada kasa-kasa ganin ta sunkunya "Lafiya lau, ga Ilhaam" ta dago tana kallon Ilhaam in "Ina yini" Ilhaam ta gaishe sa bayan ya kalleta "I am fine, very fine. How are you doing?" Ilhaam tace "Lafiya lau" ganin Yesmin na hararan ta tace "Ya aiki?" Yace "Lafiya lau, I've been in court lately, but am fine now" ya bata amsa, tashi Ilhaam tayi zata tafi Yesmin ta tsaidata "Ki tsaya mana, Ilhaam bansan munapurci" tsayawa tayi tana kallonta "Yarinyan Maāmaa ce fa itama, she's my cousin sis, ae na fada ma ba?" Gyad'a kai yayi "Muje Nike Art Gallery Rafeeq, koh Ilhaam?" Girgiza kai Ilhaam tayi, ita bazata ba "Ilhaam saida nace miki bansan irin wannan halin koh?" Tace "Ce miki yayi fa daga aiki yake, sai ki barsa ya huta ae" tsaki tayi "Ya aure ni dole kuma ya huta? Da baiyi auren ba ya wahala ne?" Saurin rike hanun ta yayi ganin ta fara masifa "Hold on My Shine, ni nace miki bazan je bane? And you told me she's our Ilhaam kar a bata mata rai, then why are you shouting at her?" Shiru tayi dan ae Ilhaam nada kayan takaici "Sai ki dawo ki zauna ae in kinada niyya, kinji dai yace miki zaije" dawowa Ilhaam tayi ta zauna dan jira take Rafeeq ya barta ita kadai da Yesmin suyi nasu, akan wani dalili zata zage tana mata ihu "Muje kaci abinci kafin mu tafi, I totally forgot ma, ka gaisa da Maāmaa?" Yace "Eh mun gaisa zuwa na, you kept me waiting" sake tashi Ilhaam tayi zata basu waje ganin sun cigaba da tadi kuma ba niyyan fitan yanzu sukeda ba "Kaga halin Ilhaam koh? In anyi magana kana bin bayanta, I told you kullum saita batan rai saidai bamu hadu ba kaqi yarda, yanzu ina zakije? Ilhaam soyayyah ne baki taba gani ba koh mey?" Ilhaam tace "Ke bazan je ba, sai kin dawo ni bacci zanyi", "Kar kije" ta fada sannan ta juya ma Ilhaam baya, ganin haka itama Ilhaam ta wuce ta barsu wajen "Yanzu mun batawa Ilhaam rai, and she's one of our best friends koh?" Tace "Karka damu, zamu shirya, muje kaci abinci mu fita danni bazan dawo ba sai gobe" dan shiru yayi yanaso ya tambaya toh yaushe zata koma gida gabadaya amma sanin yana tambaya zasuyi fada ya fasa, abincin yaci tacewa Maāmaa yanzu zasu dawo, toh har Ilhaam ta tafi basu dawo ba dan Yesmin ta rantse tareda mijinta yau ma zata kwana.


💖💫RUDANI💖💫Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang