💖💫RUDANI💖💫 65

95 24 87
                                    


2 YEARS LEAP.

Komai yana tafiya yanda ya kamata, Xeenerh ta koma school ta cigaba da karatu abunta. Ilhaam and Anwaar are living in peace dan ba gida daya take zaune da Teemerh ba balle ah kawo magani tasa mata ah gida dan ya hadata fada da mijinta. On Teemerh's side kuwa things are hard, ita batasan zaman lafiya dan yanzu Fadel ma yana wajen Mummy, taki barin sa ya saba da Anwaar balle aje wajen Ilhaam, ita kuma Ilhaam yanda tadau duk soyyayyah tasawa Fadel ma har mamakin kanta take, she concludes saboda ita bazata haihu ba ta keson na wasu, Anwaar ya rasa dalilin Fatima na distancing yaron sa daga wajen sa, yes good 2 years dole ya saba. Aameer and Ash is the same couple, shida Ilhaam kuwa haryanzu gaisuwa yake hadasu, this isn't a problem as he can now see Ilhaam happy living with Anwaar, amma yayi alqawarin Anwaar ya sake sa Ilhaam kuka bazai ma sake ganinta ba balle ta yafe masa. On the other hand Ummi had different types of attack, ita kanta damuwa takeyi da yanda yanzu basu wani bata mahimmanci, in tace ayi abu sunayi amma ita kanta tasan she is forcing them to, duk yanda tayi ta cire damuwa ranta abun ya gagara, she ended up collapsing at the hospital.


*~*~*~*

Yesmin is into depression again, her father is late and her Mums wants to forcibly get her married to Najeeb, she can't say how much she hates that guy, he was a playboy before maturity hit him and life happens, anace Abbas is nothing compared to Najeeb? Nah big lie, they are siblings and have many common things, tasawa ranta yanda Najeeb ya shiryu Abbas zai shiru. Ita dama da Abbas za'a hadata da tayi farinciki amma he is not serious with his life kwata-kwata, duk matan mey Maiduguri masu ji da kansu ba wacce batasan da zaman Abbas ba. Shima Najeeb duk a dame yake, sam ba'a barin sa yayi deciding rayuwan sa da kansa, auren sa na farko was arranged gashi yanzu wai Yesmin, duk matan duniya kawae ah wani hadasa da wannan yarinyan, ya taba soyyayyah da ita kafin ya yanke shawaran rabuwa da ita bayan haduwan sa da Teemerh, she is his cousin and he likes her sama-sama amma su ajiye maganan soyyayyah a gefe dan tunda ya rabu da ita suka daina shiri yasan ya mata ba daidai ba yanzu bata sonshi koh kadan. Asma'u kuma sheg!n kishi dan ranan sai da ta kusan yiwa Yesmin duka su Leemerh suka tare mata, ita kuma uwar sanin rights tayi filling case akanta, and Najeeb being an Assistant Commissioner Of Police ended up handling the case, toh fa yanda aka samu sauki kenan. Bilqis ma sunce ta auri Bilal (Yesmin's brother) dan matansa taki haihuwa da gangan wai saidai through surrogacy dan she is from a Christian mother and a Muslim father. Yaso biye mata amma Najeeb yace masa it's illegal, likely haram in Islam. Billy dai ta yarda zata auresa kawae dan tasa a ranta in anyi auren hala ta fara sonshi, kuma bayida matsala koh kadan yasa tadan ji dadi amma ta rasa miye nasu da yiwa mutum auren dole bayan sun san haramun ne.

Tana zaune gefe cikin hijab tana kuka a hankali dan tayi nayi harta gaji, share hawayen tayi a hankali ganin Aameer na kiranta ta dauka "Asslam, sorry I saw that online" ya fada in a calm voice "It's meant to be" ta amsa ah hankali "Allah ya masa rahama, I called Bilal and he's not picking, tell him that I and my guys are sending our condolence" tace "Zan fada masa, amma ae zaku zo taaziya?" Yace "Erm will get to arrange that, you know all are busy and I resumed work too" ya mata bayani "It's painful Aameer, I pray no one ever gets to lose a loved one" kawae tasa kuka "That is impossible Yesmin, mutuwa dole ne and every soul shall taste it nah?" Ah hankali ta fara d'aga kai "How do you feel losing different family members?" Ta jefo masa tambaya and for a moment yayi shiru, it's painful amma komai yana wuce wa "Komai zai wuce Yesmin, send my condolences to each of your family members" da toh ta amsa kafin sukayi sallama ta share hawayen ta tashi ta fita neman Bilal. Yana compound tareda Najeeb and the other men's ana karban gaisuwa. Najeeb can swear tunda yake bai taba ganinta da Hijab dogo haka ba sai zatayi sallah, ta koyi rufe kai dan dole amma sa Hijab da sauki, ganinta da Bilal yayi ne ya tashi da sauri ya tsareta kafin ta karasa cikin mazan chan "What's it?" Ya tambaya da sauri "Triple A called" tana fadi ya gane Aameer ne dan haka yake kiransa saboda sunan sa Aameer Abdallah Albaaz "Wai ya kira you are not picking, zasu zo ta'aziya hala zuwa anjima if they are not busy" ta sanar masa, duba wristwatch nasa yayi ganin lokaci, yau kwana uku da rasuwan kenan, in 30mins za'ayi addu'a and everything a gama dan Maāmaa tace zasu koma Katsina a yau dan zaman Abuja ya kare dama ta'aziya suka zo, he is their father but all the family are living separately ever since dawowan su Nigeria, he decides to remarry a young girl wanda bata wuce sa'an Bilal bafa, toh Allah baiyi auren bama ya rasu "Zamu koma Katsina a yau, all the flights are fully booked, and for the condolences muna godiya I just opened their messages and sure they are kind of busy zaiyi wuya su shigo yau" zata amsa taga Najeeb na kallonta ta sauke masa harara, she knows how she irritates him amma ya iya kallonta dan ya zageta, ta ina zata fara auren Najeeb da wannan mahaukaciyan matan nasa, duk ta dauki kishin duniya tasawa wanda bayi sonta, ita duk ta cuci kanta ae gashi yanzu wai Najeeb, ba abunda ya iya sai b'ata rai da commanding mutane "Shikenan, I will inform them" tana fada ta juya kafin maganan yayi nisa Najeeb yazo ya mata maganan banza, tana shiga taga Asmah, tana magana nefa amma ganin Yesmin ta dauki Khalifah ta b'ata rai "Ajiye mun yaro ni, kar ki shafa masa bakin jini, banda bakin jini da kin rasa mijin aure mey zai sa a badaki sadaka ma mijin wata" tana fada ta kwace danta, kallonta Yesmin tayi dama chan da kukanta, amma jin maganan ya sake b'ata mata rai, har ita Yesmin zata fadawa haka saboda wani Najeeb, no debate Najeeb is classically handsome amma tasan su waye ma sukayi dating nata? Shi kansa Najeeb ex nata ne kuma yanzu batada abunda zatayi dashi, rasa abunda zatace ta b'atawa Asmah rai tayi kawae ta share hawayen tace "Ki kwantar da hankali ba abunda zanyi da mijinki, bayi sanki ma amma duk kin bi kin damu kanki, if not because I don't love him da sai na auresa koh dan na koya miki hankali" kawae Asmah uwar rashin san raini itama ta saukewa Yesmin mari wai tayi disrespecting nata dan ita koh su Bilqis ba bari tayi ba, tadin mutunci ma batayi dasu "You slapped me?" Yesmin ta tambaya da mamaki dan ta kasa yarda "I am waiting for your worst" ta fada cikeda nuna isa, da sauri wata ah gefe ta rike Yesmin "Koh bakuda hankali ya kamata ace kun bari anyi karban gaisuwa lafiya, kuma ke Asma'u ba'a aure aka auro ki?" Kallon Maman Assad Asma'u tayi da mamaki "Oh haba?" Zata juya Yesmin ta rike ta "Sa'an ki daya Asmah, I want my father to rest in peace, banda haka ae ba wanda ya isa yamun abunda kika mun, kuma mijin naki sai an aure sa" tana fada ta wuce ta fara kuka, ga mari ga maganan banza, in badan bata shiri da Najeeb ba har wata zata mata gadara dashi ne? Tana daki tana kuka Bilqis tayi knocking "Come in" ta fada ah hankali dan batasan waye ba, shigowa tayi ah nitse "Erm.." sai kuma tayi shiru "Miye kuma?" Ta tambaya tana share hawayen "Naji abunda Asmah tayi, amma dan Allah kiyi haquri, we will get back to her later" shareta tayi jin ta sako Asmah cikin maganan ta "Yaa Najeeb yace kije" da sauri ta kalleta dan batayi expecting ba, she's not excited of course but flabbergasted, ta rasa dalilin sa na neman ta, haquri zai bata koh mey? "Hey wash your face" tana fada ta kamata sukayi toilet dan wanke mata fuskan, ita duk Yesmin ta chanja fa, kullum sai kuka yanzu, indai ba dole bane su barta da maganan auren mana kar azo ana regretting. Bayan ta wanke mata suka sauka kasa, bayi nan hakan yasa Bilqis sake hanun Yesmin taje da kanta, yana chan tareda Abbas dan an gama addu'a Bilal kuma ya fita domin yin necessary somethings in, a nitse ta karasa yanda suka matsa gefen da ba mutane "Babe it will be easy" Abbas ya fada, zai riketa Najeeb ya kallesa hakan yasa ya fasa "You look cute crying... oh I mean ugly" ya sake fada saboda neman tsokana and as expected tayi dariya "But you love me right?" Yace "Yes I do" ya amsa smiling, jin haka Yesmin ta juya ta harare Najeeb "In kun gama ki sameni a ciki" Abbas ya mata wayo ya gudu "Asmah is wrong, we are sorry" tsaki tayi jin wai defending matan nan yake "You don't even love her and we all knew it. Why hiding her scars? Dole ta fuskanshi hukunci mey tsanani. Thank God my lawyer resides here in Abuja, just by a call zaizo" kallonta ya tsaya yi ta gama "Eh zaizo, Aameer can do anything for my sake" murmushi kawae yayi, he is not in love with Asmah tun lokacin da aka musu aure, yaso ya koyi santa ma ya kasa dan batada kunya koh kadan, she is respecting no one gidan sai Mummy da Abbas danshi na kowa ne, he so much love Bilqis and Haleemah amma ita zai iya cewan ta tsane su, taya take tunanin zai sota ahaka? He has every right to reject her love. And here comes Yesmin, she is x 2 rashin kunyan Asmau saidai ita in tanason mutum bata masa, he is a living witness dan lokacin da suke soyyayyah bata ma so ransa ya baci, yanzu ma rashin kunyan nata shi kadai take wa. Bai damu da rashin kunyan da take masa ba as long as tanasan en uwan sa amma he can't marry her saboda wannan, Yesmin bata sanshi yanzu koh kadan kuma ya zama dole su hada kai su wargaza komai, and that is if she agree to "Nifa in bakada abun fada fa zan tafi. Kuma abunda Asmah tayi dole na dau mataki akai" ta fada tana juya ido saboda rashin kunya kaman ba dazu ta gama kuka wa matansa ba "Accept my apology please" tsaki ta kuma yi, Najeeb was the first to introduced her to world of love, and it failed, Najeeb shi ya fara ce yana santa tun lokacin yana gidansu a USA. They hopefully dated for good 2 years before he thought of leaving her, kowa na cewa Najeeb Yaya amma Yesmin bata fada saboda sunyi soyyayyah and she believes bazata kira saurayinta da wannan suna ba, karshen zance Bilal ma da sunan sa take kiransa balle wani Najeeb "Najeeb nayi wayo wlh, lokacin daka barni ka hango wata yarinya wai erm... Fatima koh?" Ganin bai amsa ba ta cigaba "Ka hango ta ka yanke shawaran rabuwa dani ae baka juyo ba. Nagode data koya maka hankali and you ended up being forced to a marriage da wancan mahaukaciyan abun. I am a victim of love and the first time that Fatima ruined my happiness, and now? Kana tunanin zan aure ka? Aa kayi kuskure" ta fada hankali kwance dan yanzu inda zata ga Teemerh sai ta mata duka, she then met Anwaar and he somehow started to love her taje tayi hauka ya daina santa, Aameer yazo kawae taji wae Aameer yayi aure sai yanzu azo ah wani hadata da ex ae taci baya, tayi alqawarin sa Najeeb kuka yanda ya sata, Abbas zata komawa, at least zaiji haushi ae "Yesmin, Fatima is married and no way am taking her back" yayi saurin defending kansa, dan kallonsa tayi ta wani bata rai, koh bai tambaya ba yasan bata yarda ba "She married Anwaar Albaaz, your Aameer's cousin righ-?" Tun bai karasa ba ta durgusa tasa kuka, ita Teemerh ta rantse sai ta rabata da komai kenan, tasan Anwaar ya auri Fatima bayan sun daina soyyayyah dan har ya auri that girl Ilhaam that he loves so much, amma why does it have to be Fatima? Yarinyan data fara sata kuka, taji ya auri Ilhaam kuma yana sonta sosai amma bataji zafin auren Ilhaam da yayi kaman wannan ba. Ita yanzu maganan rasuwan Baba a gefe ma, tasan kowa zai rasu kuma zata masa addu'a amma koh ta tafi Katsina saita dawo koh dan koyawa Teemerh hankali. She knows Anwaar will never choose her over his wife but she's someone Anwaar loves first. Tasan dole watarana yana tunawa da ita, it's now between her and Teemerh na hanata auren Najeeb daga farko, tasan ba ita tasa Anwaar rabuwa da ita ba dan bata isa ba, amma meyasa zata auresa? Ita auren Fatima da Anwaar yayi yafi mata komai zafi dan ta lura Fatima ta dage sai sun hada ex, inda a USA take da yanzu ta cika form cewan an aure mata saurayi dole su rabu ma "What's wrong please?" Taji muryan Najeeb, kafin ya sake ce wani abun ta tashi da gudu, girgiza kai yayi dan baisan mey kuma yace mata ba.


💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now