💖💫RUDANI💖💫 59

103 25 71
                                    


MAIDUGURI

Mum and Yaa Mariam zaune suna tauna maganan Ilhaam dan ita Mum ah zahirin gaskiya taje tayiwa Malami bayani kuma ya tabbatar mata da cewan indai ba aljanu ne suke bin Ilhaam ba toh fa tabbass sihiri ne jikinta "Toh ke kuma har kin wani yarda?" Da mamaki Mum ta tsaya kallon Yaa Mariam dan ta tabbatar zaman k'asar waje ya maidata haka, banda haka aljanun ne ba koh shirin ne ba'ayi? "Yaya amma dai kinsan duka biyu gaskiya ne" ta tabbatar mata "Toh yanzu dai kinsan ba bamu yarinyan nan zasuyi balle akaita wajen mey maganin aljanu ya tabbatar mana bako?" Gyad'a kai Mummy tayi "Kuma koh na kira Sabeerah ba dauka take ba, haryanzu bata bar fushi da abunda bai kamata ace tanayi ba" Yes Yaa Sabeerah Yayar Ilhaam ce kuma ita tasan da zaman su Mummy amma sam bata mu'amala dasu, shiyasa itama bata damu dace musu Ilhaam tayi aure ba, Yaa Mariam batace komai ba tadau waya ta kira Sabeerah, saidai itama har ya gama ringing bata dauka ba, daurewa tayi ta sake kira sai da ya kunsan gamawa shima kafin ta dauka "Mun yini lafiya Māamaa?" Sabeerah ta fadi ah nitse "Lafiya qlau, ina Ilhaam? Yasu Alameen da matan sa?" Ita Sabeerah tasha mamakin jin wai tasan Aameen yayi aure, tasan Aameen is not in contact with this woman, toh taya za'ayi ya fada mata? "Who told you that?" Ta tambaya da mamaki "Aliyu told me" Sabeerah sighed, Thank God ta cewa Yaa Abu ta fada musu maganan auren Ilhaam, inda tace bata fada ba da yanzu sun sani, her sister will never go near these people, she has a family and that is them-the Albaaz "Ya Ilhaam?" Maāma ta sake tambaya "Tana lafiya, kunsan tana wajen Ummi ae, ni kuma ina gidan aure" ta hade karya "Toh ga Aseeya zatayi miki magana, Allah kuma yasa ki fahimceta" shiru tayi dai, dan suka dauko mata wani shirme kashe wayanta zatayi, jin tayi shiru tasa a speaker ta bawa Mum "Ina yini?" Ta gaidata dan dole "Lafiya Sabeerah, ya gida da yarinyan?" Tace "Tana lafiya" nan fa Mummy ta fara zayyana mata, tunani ta fara bayan Mummy ta gama maganan, toh waye zai wa Ilhaam asiri? Kuma akan miye aljanu zasu bita, kawae ta kashe wayanta, after much of pleadings ta message ta kirasu dan kanta "Ya za'ayi tazo ah kaita wajen Malamin ya ganta?".... "Dama ni nasani ae, kawae kuna neman abunda zai sa tasan da zaman kune, and believe me hakan bazai faru ba, Ilhaam is damn happy with her life right now" ta fada in a calm way bawae da rashin kunya badai "Sabeerah ki daure ki fahimceta, matsalan Ilhaam namu ne kuma naki ne" Maāmaa tasa baki "Indai akwae gaskiya cikin maganan ya bada maganin da za'a bata kawae, ni nayi alqawarin zuwa na karba Ammaah wlh Ilhaam bazata zo ba" ta shaida musu, dan ita daya bayar dakar ya bayar duk daya dan ita Allah nagani bata yarda da koh wani maganansu ba "Shknn tunda kince haka, zan masa bayani asan yanda za'ayi, amma ae in ya ganta zaifi gane matsalan nata" Sabeerah tace "That's the only thing I can do".... "Toh duk yanda mukayi zakiji" nan sukayi sallama, ita Sabeerah tasa ah ranta koh sun sake kiranta bazata ba, ana zaune qalau kam baza suce anyi wa Ilhaam asiri koh wani abu ta yarda ba "Allah ya shirya mana Sabeerah" Maāmaa ta fadi tana dan murmushi "Yaya amma muma fa da laifin mu, koh yaran namu bamu bari sunsan juna ba, ni harnayi zaman Abuja ban taba gwada musu sunada alaqa ba, shi Najeeb ya fara neman yarinyan gidan ma naqi abun na hada shi aure da Asmah, ke kuma tunda kuka wuce chan baki sake waiwayan kowa ba, saidai kizo ah shekara sau daya koh biyu" taji maganan ya shige ta amma ae ba yanda ta iyane "Maāmaa kinga Najeeb koh?" Yesmin ta shigo da gudu, Yes she's our Yesmin-Aameer's ex gf, ita dan rashin kunya ma kowa na cewa Najeeb Yaya ita bata fadi "Najeeb dai yayanki ne amma duk kin bi kin raina sa wlh, gwanda yamun maganin ki ae" Maāmaa ta amsa, Yesmin bata damu ba dan tasan right inta, Najeeb na dukanta zata tabbatar an bi mata hakkinta ah court, ita ta rasa mey ke damun Nigerians in nan dasan shiga hidiman daba ruwan su, banda haka miye damuwan sa da ita da zai wani dage saita sa dankwali, tsaki tayi batasan tayi ba tuna abunda ya mata "Sorry" ta fada ganin both Mums nata na kallonta karma suyi tunanin dasu take "Yawwa, Maāmaa zanje Abuja gobe, akwae wanda nakesan gani" sake baki Mummy tayi ganin irin tarbiyan Yesmin "Uban waye zakije gani? Kuma da izinin wa?" Mummy da bakinta baiyi shiru ba ta tambaya, wai fa tayi karfin haline ma dan ita sam batada fada "I am meeting my boyfriend" ta bata amsa sannan ta zauna kusa da ita "Yanzu ke har wani boyfriend kikeda?" Sake bin kanta da kallo Yesmin tayi "Mum what do you mean? Banida kyau koh mey?" Girgiza kai Mummy tayi "Mu ae anan ba kyau ake dubawa ba tarbiya ake dubawa" wani rolling eyes tayi tunawa da pictures na Aameer data gani dakin Leemerh "Taya ma zance wa Leemerh Aameer is my bf kuma taki yarda? I am taking her to his house tomorrow" ta fada zata tashi Mum ta zaunar da ita "Wani Aameer?" Ta tambaya da tsoron kar tace Albaaz "Aameer Albaaz, Maāmaa kinsan da zaman sa kekam ae" tayi maganan tana kallon Maāmaa hakan yasata dan murmushi "Ba yanda zaku toh, kuma zansa Najeeb yasa muku ido" Mummy ta hanata hakan yasa ta tashi tana buga kafa "Allah gidan nan akwae takuri, gaskiya nikam zan wuce Katsina, I know my family will welcome me cheerfully" tana fada ta tashi abunta "Yaya gaskiya tarbiyan yarinyan nan da sake, yarinya ba rufe kai ba sallah akan lokaci ba salati? Irin su aljanun suke nema ae, duk irin su masu sakaci akewa asirin" Mum ta fahimtar da er uwanta "Hakane, amma kinsan kowa da halinsa ae, shi Bilal ae ba haka yake ba" Maāmaa ta defending kanta "Ya Bilal da matansa? Haryanzu dai bata haihu ba tukunna koh?"... "Kinsan ta maqalewa boko ae" ta mata bayani nan tace "Allah ya kawo zuri'a dayyiba" Maāmaa ta amsa da Amiin. Yesmin kuwa komawa tayi wajen su Leemerh aka daura musu, ganin Leemerh taki daina karyata ta ta ciro waya dan nuna musu pictures nasu tare "Kinga, saboda raini irin naki, ni na miki kama da wanda zata miki karya, kuma banda rashin kunya bakiga yana following duka socials ina ba?" Ta wani hade rai, bayan Leemerh ta karbi wayan Billy ma tasa kai "Hey, don't tell me, gashi kuwa ashe gaskiya kike fadi" kawae tasa ihu tayi hugging nata "But Yesmin, Aameer is married" Billy tasa baki hakan yasa sukayi breaking hug in "Kinsan miye? Nifa aihini bashi ne saurayina ba" tana fada duk suka zuba mata ido harda gyara zama "Anwaar was my boyfriend, I love that guy before he finally think of leaving me" bude baki Billy tayi, wai har akwae wanda zai iya rabuwa da Yesmin? "Who's Anwaar? Kuma mey kika masa?" Ta bata double questions lokaci guda "Anwaar is a Doctor, a very private human dole bazaki sansa ba" sai kuma ta wani lumshe ido ta kwanta ganin suna san jin labarin "Allah sai kin karasa mana" Billy tasa hanu ta dagota "Toh kunce bakusan Anwaar ba, how will the story amuse you?" Leemerh tace "Woah, Allah naganesa, I saw one video clip online shida Aameer ah hospital trying to fight each other" ta fada tana so ta tuna yaushe ta gani, all she knows is that ya kwana biyu, zai iya kaiwa 2 months koh fi "Yawwa, kin gane sa yanzu" Yesmin ta amsa bawae dan taga videon ba, saidan sanin su da tayi, tasan confirmed su Leemerh ta gani "Toh continue" Billy tayi pleading kafin tacigaba "He was my boyfriend" Leemerh tace "Kin fadi wannan" tace oh "Kunsan yanda nasha wahala kafin ya fara sona? Amma wlh tunda ya fara sona bai kuma san wata ba, even though he loves me 20% out of 100, I can say Anwaar is the best guy I've ever met, but I love him the most danni duka 100 nake masa" ta fada kaman tayi abun gwaninta "Toh yanzu fa? Yana sanki yakai 80?" Leemerh tayi saurin tambaya "No, I heard that he's married to two wives fa, I pity the first one dan Allah month ne tsakanin ta da amaryan" da sauri Bilqis ta matsa "Tabb, wlh he's not a nice guy indai hakane, how can he get married for the second time in one month? Hauka ne abun? Ita ma first wife in nasa wawiya koh kuma dama chan ba ita yakeso ba" Ta fada tana girgiza kai Leemerh na goya mata baya "Toh miye ah ciki? Wlh nima if am the first wife zan yarda yayi aure indai zai soni, ina ruwana da wata, Allah yana santa sosai fa" ta musu bayani "Kekam ae banza ne, ba mara ban ki da first wife in nasa, banda haka ita kishiya ina ruwan ta da san da yake miki? Tsaf zata shiga tsakanin ku" for a moment Yesmin ta tsaya tunanin rayuwanta, she would like to meet Ilhaam and ask her how she copes da kuma yanda akayi Anwaar yabar halayen banza "Toh dama Yesmin kema dai ba sanki yake ba" Billy ta fada ganin tayi shiru "Yanzu kam bayi sona, he loves one person, I don't even know how the second one is coping, erm... Fatima" ta fadi sunan bayan ta tuna "Why?" Tace "Ohh, in fada muku rabuwa yayi dani saboda one night party da nayi attending kawae yace mu rabu" Billy tace "Toh kema Yesmin mey ya kaiki?" Dan juya ido tayi "Duk ke bakiji ki tambaya ya nayi coping bayan rabuwan mu ba sai dalilin zuwana? Bansan haka" ta dakatar mata, wai fa ah haka Billy ke mata yanda taso saboda sune age mates, Leemerh na farawa take tsaidata dan gani take she's one year older than her, itafa bata girmama manya amma ita tanasan girma "Toh ya kikayi bayan rabuwan ku?" Tace "Yawaa magana kenan, amma fa ba yau za'a karasa ba, some other time" tana fada ta juya ta kwanta abunta, the first time after years when she realized that she still love Anwaar amma no way he's taking her back.

💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now