💖💫RUDANI💖💫 95

46 21 62
                                    


Tsakani da Allah Halimah ke kuka wae ta gane Aameer is into drinking unnecessary somethings "Toh ke naki ah mey? Sai ki fada mun ya relation naki dashi da zaki wani dage kina kuka" Asma'u data bata haquri taki haqura ta fadi wannan dan b'ata mata rai "Toh Yaa Asmah he is damaging his health fa. That was why some of his pictures look inebriated" tayi maganan da shaking voice tana share hawayen "Toh wae ke waye yace miki yana shan wani abu?" Saida tadan yi shiru na seconds kafin tace "Jiya wajen taron chan naji wasu suna maganan, they are new faces kuma" Asmah tace "Kikaji wasu suna gulman dai, maganan daban gulman daban, toh sa damuwa ki mutu kibarsa tunda shi kesha, ke kuma sai kiyi masa jinyar. Aikin banza" hararanta Leemerh tayi ganin itafa wannan ba'a dadewa ana mutunci da ita, toh tun wuri su tattara su bar musu gida, masifa dasan girman Asma'u kullum karuwa yake "Ke kenan baza'a nutsu ayi maganan mutunci dake ba? Sau nawa zance muku ba sanshi nake ba? He is my role model" ta fara mata bayani amma tun kafin yayi yawa Asma'u ta tsaidata "In kinaso mu san ba sanshi kike ba sai ki daina haukan ki nemo miji kiyi aure, wawiya kawae" ta fada sai kuma ta hade rai ganin Najeeb ya shigo, banda rainin wayo har ita zaice zaiwa kishiya kuma wae Teemerh "Baki shirya ba haryanzu? Do you want your siblings to wait till night?" Kallonsa Leemerh tayi sannan back to Asma'u da tayi shiru taqi kallonsa saboda ta rasa da wanne zata fara masa "Ke kuma kukan mey kike?" Ya tambayi Halimah ganin yanda idonta yayi kumbura na musamman, saurin share sauran hawayen tayi ta fara girgiza kai kafin ma yasan dalilin kukan nata, barin tambayoyin nasa yayi yabi bayan Asma'u ganin tayi wajen Mummy, Allah dai yasa karta cewa Mummy komai kawae "Toh wae akan wani dalili in ma auren zakayi kace sai ita Fatima? Duk halin da Ilhaam ta shiga ba sanadin ta bane? Saboda kai mugu Allah bai sa maka tausayin en uwa ba koh Najeeb? Toh ae sai ka aureta na gani" Mummy ta fadi bayan Asmah ta gama maida mata abunda ya fadi jiya, kuma Najeeb yaki tsayawa suyi magana akai "Mummy yarinyar tausayi take bani, kinga-" saurin katse sa Mummy tayi "Sannu uban tausayi, ae kaida tausayi na haifo ku tare" Asmah na gefe ta sauke ido tanajin dadin yanda ake masa fada, ae ita yanzu wahalanta ya kare shine next "Kiyi haquri Mummy, daman I wasn't serious about it" ya mata bayani, sai lokacin Asma'u ta kallesa "Ina ruwana da seriousness naka koh Aa? Asma'u dai tayi kokari da haqurin zama dakai, kuma dukda haka baka appreciating?" Dadi sosai itafa Asmah taji dan dama karya Mummy ta bata laifi kan Najeeb, tasan Mummy na santa tun ba yau ba, komai tayi kuma saidai kawae tace karta sake, shiyasa yanzu take kiyaye fushin Mummy "Kiyi haquri Mum" ya sake maimaita wa "Kiyi haquri kinji Asmah? Jeki shirya karki damu" Mummy ta fada hakan yasa Asma'u tashi ba tareda ta kallesa ba ta fita "Mum, amma koh lokacin da kikace na auri Asmah, kince zan iya auren duk wanda nakeso bayan ita, tunda anyi auren baniso ae" Mummy tace "Anyi auren bakaso, yanzu kuma fa? Ka rantse mun da Allah haryanzu baka san auren" shiru yayi ganin yanda yau Mummy ke fada, ba halinta bane "Kuma ah auren ka rasa wa zaka auro sai Fatima? Toh Allah ya shirye ka tunda mafad'a ka rasa" saurin girgiza kai yayi "Kiyi haquri" ya sake maimaita abunda yake fada tun dazu "Kaje ni karka cikani da haquri" ba musu ya tashi ya fita sai ganin Abbas yayi da headphones da alamu dai waqa yakeji, girgiza kai yayi ya wuce kawae dan ba yanda za'ayi suyi ma Abbas aure da wa'innan halayen nasa. Koh da yaje part nasu Asmah harta shirya shi take jira ma "I am sorry Asmah, I knew the love you gave me is which I will never buy. I want such a girl, who can see my heart's desires, all the dreams, and all the colors come alive lately. Even today I love her the same, and not because I haven't found anyone else, but because I don't get any time to love her. You are that girl Asma'u, I love you so much" kallon sa kawae ta tsaya yi jin yanda yake magana perfectly, if not the best husband what? "Ka sauke girman kan?" Ta tambaya in a soft voice tana tunanin Najeeb ne dagaske koh Aa, bai cika kuluta in tana shirmen ta ba, silent treatments yake bata kuma yafi ci mata rai, she had enough of Najeeb and his sisters, yanzu harta fara haqura da wasu abun "Na sauke" ya amsa yana dariya hakan yasa tayi dariya itama "Kullum ina sanka nikam, and I love your siblings too, kawae dai sune suke mun rashin ji, they are not respecting me as their sister in law" tayi maganan flatly kaman mey jin kunyan magana "And you are not the kind that overlooks? Allah ya shirye ki" girgiza kai tayi "Albarka zaka samun" ta sake fada ah hankali saidai yanajin duk abunda take cewa "Allah ya miki albarka, can't believe you will be the wife I had been praying for. I love you" ya maimaita, sosai take jin dadi harda tsalle "Amin, thank you so much and I love you too" tayi saurin hugging nasa "Can we?" Ya tambaya after breaking the hug "Yea" ta amsa sannan taja hanunsa suka fita.





💖💫RUDANI💖💫जहाँ कहानियाँ रहती हैं। अभी खोजें