💖💫RUDANI💖💫 94

53 23 76
                                    


Aunty Sham ta dawo daga Chad amma ta dawo da labari mara dadi, their mother is dead dan itama sai randa ake uku taje. Tayi kuka kaman ba gobe dan ita kadai ce ta rage musu dama toh gashi sun rasa ta, abun haushin wae an rasa waye zai fada musu "Mu kam munyi asara" kadai take maimaitawa "Aunty, dan Allah kibar ce kunyi asara. In kunyi asara mu kuma fa?" Teemerh ta tambaya da damuwa ah fuskanta, ta rasa da wanne zataji ma, da rasuwan ne koh da auren dasu Anwaar suka sake, it hurts, tafi kowa farin cikin sake auren da sukayi amma abun na mata ciwo, yanda Anwaar ya sata ah gefe kawae take tunawa ta fara kuka, tayi kuskure amma ya yafe mana dan Allah ita ya maidata dakinta, tayi alqawarin zaman lafiya da Ilhaam, ba Ilhaam kadai ba da kowa ma, ta kirasa yafi ah tsaya irgawa amma bayi daukan wayan ta, he hasn't block her ah koh ina saboda koh time in blocking Teemerh bayida amma tasan ta rasa Anwaar har a bada, in ya tafi bayi juyowa "Munyi asara" Aunty Sham ta sake maimaitawa "Aunty bamuyi ba" Teemerh ta sake hanata fada "Munyi asara mana, ina amfanin abunda mukayi yanzu? Na rasa kowa nawa fa" Teemerh tace "Baki rasani ba Aunty, kuma akwae Yaa Xee da Habeey. Slowly su Mallah zasu yafe miki tare da Abba suma" ta fara consoling Aunty Shamsiyya "Koh ya yafe mun miye amfanin abun Fatima? Saki uku yamun ba komawa. Duk akan shi na wahala gashi ya rabu dani" Teemerh tace "Yafiyan shi yafi komai amfani Aunty, saboda in an yafe kinga hakkin wa'inda muka zalunta ya sauka kan mu, kuma kinga nima sakin nan an mun shi, kuma bayida niyyan maidani" pausing tayi kafin ta cigaba "Kinga abunda mukayi wa Ummi ta yafe wlh. The woman is sooo good. Allah dai yasa Anwaar ya maidani kawae saboda I will be obedient har karshen rayuwata" ita kanta da ta fada sai da tayi small laugh sanin bata gaban Anwaar koh kadan, saurin daukan waya tayi ma dan sake masa wasu warm messages in dukda tasan koh budewa bayi yi. Tana fatan dai koh by mistake ya budesu, kawae dai zata cigaba da rokon Ilhaam da Ummi, idan alkhairi ne Allah yasa ta koma, ita tasan komawa gidan Anwaar alkhairi nema. How she sacrificed everything to live with someone who doesn't love her was her poorest decision, lokacin daya fara santa kuma lokacin ya tsaneta. It hurtssssss. "Ke dan Allah ki cire yaron nan ah ranki, kinsan dai ba yanda za'ayi ya maidaki koh? Kawae ki manta shi muji da matsalolin dake gaban mu. Nikam ma ina zan sa kaina" sai kuma ta fara kuka, Teemerh dai haquri kawae take iya bata dan ita tafi Aunty Shamsiyya matsala "Aunty, zaki iya zama anan fa kinsan Daddy bayida matsala tunda dama anan kike. Shidai yace zai kara aure. Allah yasa ya auro mey mutuncin da zata kula dashi" Teemerh ta fada dan ita yanzu tunanin Daddy ma kadai shine ah ranta, burinta ya samu farin ciki bayan duk abunda ya faru, ya rasa abubuwa da yawa bayan sunan sa daya b'aci "Toh yanzu Fatima in matar nasa tace bazan zauna ba ae kinga dole na tafi tunda gidan tane" kallon ta Teemerh ta tsaya yi kafin tace "Gidanta ta ina? Ba wanda ya isa ya kore ki tunda ke kadai nake da yanzu. Kinsan Anwaar ya sake auren Ilhaam koh?" Shamsiyya tace "Koh jiya ma kin fada mun fa. Allah ya basu zaman lafiya ke kuma ki dage da addu'a. Allah ya karbi tuban mu" da Amin Teemerh ta amsa ah hankali amma ta kasa manta abun ne fa "Kije kisa ciwo wa kanki ki mutu, cigaba da rayuwan sa zaiyi ae shi, yaushe dawowan ki daga asibiti? Ni wlh na zata ciki gare ki ma" ware ido tayi jin abunda Aunty Sham tace, in akace tanada ciki ae sai su tambayeta cikin waye, ita da takeda worst relationship da Anwaar, yes he started to love her amma ta b'ata komai, kuma duk wannan ah gefe ita fa da kanta ta lalata mahaifanta, gani take ae ta haifa masa Fadel no need ta sake wani haihuwa, he would love her tirelessly ita da yaronta in yaga su kadai yake da, shiyasa ta fara shan maganin hana haihuwa. Ita yanzu ta gane batada wayo ma, in kana mugunta ae sai kayiwa kanka ma. Ganin tun dazu Aunty Sham na kallonta tasan jiran amsa take "Ba ciki bane Aunty, but am regretting it now, inda ciki ne da yanzu nasan komai ya dai-daita, he loves kids more than the way he loves himself. Nasan da yanzu na koma daki na" kuka ta fara tun kafin ta karasa, ita duniya ba wanda ya cuci kansa kamanta "Allah shi kyauta" Aunty Sham da bata gane zancen Teemerh ba ta fada.


**~***~~**~~~**

Komai ya shiryu yanda ya kamata cikin garden room nasu, abun dai sai wanda ya gani dan mugun shiri Ashphert tasa ayi "Ashphert yanzu everything is ready za'a iya kiran Aameer koh?" Xeenerh ta tambaya "Yeah sure ki kirasa yanzu" matsawa gefe Xeenerh tayi dan kiran Aameer saboda wajen da hayaniya, sake kallon yanda wajen ya cika tayi sannan tayi murmushi dan kusan duk wanda suka sani sunyi inviting nasa kuma ba wanda yaki zuwa "Yaa Aameer where are you?" Xeenerh ta fada ah dame "Mommy Affan lafiya kuwa? Don't panic please"ya fada jin yanda take maganan "No ba lafiya ba, can you come home now?" Ta sake fada duk ta daburce masa "I don't think so saboda akwae abunda nakeyi yanzun and it's very important" ya fada factly "Please, Ashphert ce batada lafiya kuma taki zuwa asibiti wai kai kawae takeson gani, please come soon" Aameer exclaimed "What?! Amma na fito gida lafiyanta qalau" Xeenerh tace "Nima yanzu zuwa na and I found her shivering da alama akwae fever a jikinta" Ashphert data biyota sauran kadan tayi dariya "Okay I'm coming right now, ki kula da ita kafin na dawo" murmushi tayi jin ta convincing Aameer cikin sauki har zai zo "Okay am hanging" ta fada kafin ta kashe "He is coming guys" ta dau mic ta fada musu nan kowa ya fara murna, saida sukayi timing nasa kafin suka kashe lights in wajen aka ba kowa haquri. In less than 4mins sai ga Aameer ya karaso gidan, tun daga gate ya fara ganin motoci hakan ba karamin d'aga masa hankali yayi ba dakyar ya karasa ciki, ba yanda bai duba ba cikin gidan, Xeenerh kuma ya kira wayanta taqi dauka, ganin wajen garden da mutane ya mugun shan mamaki kuma ya damu, gashi ya kasa tambayan securities in gidan abunda yake faruwa, daurewa dai yayi ya shiga amma ba haske wajen, yana kokarin kunna lights switch in yace "Princ-" kafin ya karasa yaga lights sun kawo sai mutane daya gani "Happy birthday to you" suka fada in chorus, mamaki ya tsaya yi danshi ce masa akayi matar sa ba lafiya, da sauri Ashphert tazo taja hanunsa dan kuwa taga ya tsaya ya gagara karasowa "Happy birthday My King, My Yaa Aameer. I love you" ta fada sannan tadanyi dagel ta mishi peck a forehead nasa, he couldn't help but to smile "Thank you" ya fada da smiley face ganin how she tried, wajen yayi kyau sosai ga different types of cakes, sure Ashphert is aesthetic. Gaisawa ya fara da wasu daga cikin mutanen dake wajen dan gaisawa da duka bazai yiyu ba, waqa akasa sannan wanda suka iya rawa suka shigo dan ayi dasu. Teemerh dai na gefe dan dalilinta na zuwa dan taga Anwaar ne koh Allah zaisa yayi noticing nata amma saidai kaman baizo bama, Ahmad kuma ya dage wajen rawa, Abbas ma tanan yafi kauri, shi ah duniyan nan ah barsa da jin dadi kawae, rawa sosai mutane keyi yanda Ash taja Aameer gefe tana fada masa how much she loves him, saidai shi ya lura ba Ilhaam, yanaso zai tambaya amma ta dauko wani zancen hakan yasa ya manta "Nida Nihaal muna missing Papa, kullum cewa kake aiki yama yawa" murmushi yayi jin sunan Nihaal, tana bacci yanzu haka yasani, yanaso ma ya dubota amma bayiso a ganta balle ta shiga forum, dan tunda aka haifeta banda en uwan kusa ba wanda zaice ya tab'a ganinta, wasu cewa suke basu san mey Ashphert ta haifa bama "I love you more my Princess, this is great" ya fada da warm smile, bayan an gama rawa mutane suka fara kawo masa present nasu "Thank you, thank you" kawae yake cewa, anyi cutting cake yaba Ashphert, zata bashi kenan sukaji muryan Ilhaam dan wajen yayi shiru da kuwa baza suji ba "Happy birthday Yaa Aameer" ta fada da sauri sannan ta karasa Anwaar na biye da ita hakan yasa Aameer fasa karban cake in da Ashphert ke bashi ya tsaya jiran Ilhaam ta karaso "Happy birthday Papa" ta maimaita "Thank you Baby, but a present from you is compulsory" ya fada gabadaya attention nasa kanta "Yes you can't believe it" ta fada very excited "What?" Ya fada eager to know what she is up to, key in mota ta ciro ta bashi "A car" ta fada tana basa, dan rufe ido yayi ya bude "Oh wow" ya fada sannan ya karba cikin farin cikin kyautan da Ilhaam ta basa "And you know the most exciting thing?" Girgiza kai yayi "No what? Tell me please" ya bukace ta "I have got the same car too" ta fada zata fara rawan kai ya katseta "Ilhaam you are so sweet. Come and take a bite" yaja hanunta suka karasa wajen cakes in, bata kula ba taji an sauke mata mari "Ouch" tayi saurin fada kafin ta rike wajen, ba mamaki koh kadan fuskan Ilhaam ganin wanda tayi marin amma saida hawaye ya fara neman hanyan sa "Ashphert bakida hankali ne?" Aameer yayi saurin tambayan ta ganin marin da ta bawa Ilhaam "Are you fine?" Aameen dake kusa da Ilhaam yayi saurin tambaya banda Anwaar dake gefe hanun sa cikin gashin kansa, shi ah duniyan baisan tashin hankali, kuma da matan sa da qanwar sa? It's a No "Duk saboda ita ne kake duka wannan Aameer?" Ashphert ta tambaya tana kuka itama "Duk wannan abun da nayi ya tafi a banza kenan saboda gift nata guda daya? Im very disappointed" ta fada kukan nasan fin karfinta "Dalilin da yasa kika mareta kenan?" Aameer ya kuma tambayan ta dan bai ga dalilin marin ba, kowa ya kawo gifts ya karba amma sai kar ya karbi na Ilhaam? Saurin tsare abun Anwaar yayi "Look Ash, Ilhaam is sorry please" Anwaar ya fada sannan ya kama hanun Ilhaam dan su fita aka bisu da kallo "You people should leave please, wannan abun duk bayida amfani" Ashphert ta fada sannan tayi waje itama. Xeenerh da Teemerh aka bari suna bawa mutane haquri sai Amrah dake tayasu, Yesmin, and Billy were not present wajen taron. Bayan an gama watse wa ne Najeeb ya tsaya da Teemerh suna magana saidai duk hankalin Asmah na wajensu "I knew it isn't right asking you to marry me now tunda iddah kikeyi. But I would like to, in kin gama" hawaye kawae taji ta fara, how Anwaar made her a trash, yazo amma koh kallonta baiyi ba, bata tunanin yasan tana wajen ma dan suna zuwa abun ya faru suka tafi, tasan inda yasan tana wajen ma bazai zo ba, Najeeb kuma tasan tausayi take basa yasa yace haka, kuma tasan ba yanda za'ayi ma ah bari ya aureta bayan Ilhaam er uwansa ce kuma ita taja wa Ilhaam komai "I knw you don't love me now, tausayi nake baka" ta fada tana share hawayen, kallonta ya cigaba dayi dan ah gaskiya yanzu bayi santa "Bayan Anwaar ya rabu dani na gane bani sanshi, na gane kawae kishi nakeyi da Ilhaam yasa na fara sanshi tunda. I want to be loved the way Ilhaam is loved by Anwaar and Aameer shiyasa, sure na aure sa and he gave me care and some love. Yanzu gani nake am not worth any love. Anwaar bazai ma maidani ba saboda na cuce sa, I want my own family Najeeb" sai kuma tayi pausing ta rasa mey zata ce next "Kin yarda bayan kin gama iddah zamuyi aure?" Sake kallon sa tayi kawae tana regretting rayuwanta, actually yanzu Najeeb bayisan Fatima, shi Asma'u ma ya fara so yanzu, he is now thanking Mummy because she made the best choice. Asmah tana sanshi sosai kishi kawae ke damunta kuma yasan matsalanta, matsalan daga wajen sane ma saboda he is not securing her, gani take any time zata rasa shi, but here is Fatima, sunan gidan su ya b'aci kuma mey aurenta zaiyi wuya, and Ilhaam from the other side, suna so Ilhaam tayi farin ciki bayan duk abunda ya faru da ita, ba probability koh kadan cewan Anwaar zai maida Teemerh dan yanda bayi koh san ganinta amma in tsautsayi yasa ya maidata Ilhaam will not be herself again, shiyasa ya yanke shawaran auren Fatima "But I love my wife, and to respect her is a must. I married her saboda Mummy tace, family friend ce. I don't love her from the start, amma tana kokarin yimun biyayya, her relationship is not good with my siblings, amma komai zai gyaru ah hankali" sure Asma'u na san kyautata masa saboda ita tana sanshi amma shi ganin dama yake mata, so kawae yakeyi ya b'ata mata rai saboda yasan ita tace tanasan shi har yakai ga maganan aure, she's schooling oversea amma yana aurenta yace ta dawo Unimaid dan ya qona mata rai amma bata damu ba, Daddy yayi magana Najeeb yace Aa, Unimaid Asmah zata cigaba kuma haka akayi. Sai yanzu da suka dawo Abuja ta dawo Baze, yanzu ya fara santa kuma yace ta zabi duk yanda takeso tayi karatu amma taki wae zata karasa Baze tunda sauran shekara da yardan Allah, ya lura she is losing interest kan duk abunda ya kawo, he is not blaming her because she tried but he messed up. Shiru Teemerh tayi jin duk mey hankali will want his first wife to be respected, yanzu ta gane Anwaar bayida laifi in ya nema wa Ilhaam respect, ita kam ae ta shiga uku tunda ta bari aurenta ya kare "I have a beautiful girl in mind da nakeso na ba Abbas" tayi saurin chanja topic of discussion in "Who is she please?" Najeeb yayi saurin tambaya "Amrah, she is my friend and sister'n Ahmad ce" dan shiru yayi jin wae qanwar Ahmad, kai bazai yiyu ba "Wlh Amrah is good, ba ruwanta da abunda Ahmad yakeyi koh nakeyi" ta masa bayani gane kiran sunan Ahmad da tayi ya b'ata komai "Oh is she not married yet?" Ya tambaya, yasan dai koh da Abbas ya yarda dole ayi bincike kafin aure, in bai yarda ba kuma shknn "Batayi aure ba ta tsaya karasa karatu kasan mu bamuyi university ba" ta fada tana dariya "Ae kuwa in munyi aure ya kamata kiyi" murmushin karfin hali kawae tayi "No nifa yanzu banda interest a karatun, Anwaar ma ya tab'a sama mana admission nida Ilhaam a France amma munqi" ta fada tana yatsina fuska, ita mugun bin na Ilhaam tayi akan Anwaar "And this time around is not Anwaar but Najeeb, kuma sai na tabbatar kinyi abunda ya dace. Sai ki fada mun wani country kikeso na kaiki?" Tace "Shikenan that aside, in munyi auren sai ayi wannan but for now muyi magana Abbas in" itafa tana kaucewa ne dan gani take kaman Anwaar zai sake kulata "Don't worry zan fada masa" suna gamawa ya tashi. Ahmad kuma da dama tuntuni yana hankalce dasu ya karaso "Teemerh mey kikeyi da wancan guy in?" Tace "Aure na zaiyi kuma I gave out my consent" ta masa karya "Amma bakida hankali koh? Kuma shi banda jahilci ina shi ina neman auren mace mey iddah?" Tsayawa kallon sa tayi tanaso taga wa yafi sanin addini, Najeeb ae cewa yayi inta gama iddah, he said nothing wrong duk cikin maganan su, he doesn't even mention something like love irin yace yana santa Aa, and he makes sure to lowered his gaze"Rashin hankalin mey nayi?" Ta tambaya dan neman sani "Kin san cewa ni nake sonki kuma kika yarda ma wani?" Tsaki tayi tasan maganan kenan kullum, shi yanzu mey yakeyi da yake wani kokarin blaming Najeeb "Ahmad yaushe-yaushe kayi aure? Beside Sarah qawata ce ni yanzu bazan sake auren mijin qawata ba indai Anwaar bai maidani ba" kallon yarinyan nan yakeyi da mamaki, su da zasu hadu su gyara kuskuren da sukayi ta hanyan yin aure kuma tana ce wani daban zata aura ma "Toh kuma baza ki auri Najeeb ba ni zaki aura. Mu gyara kuskuren mu koh Allah zai sa su yafe mana" tace "Ka hanani auren nasa" ta fada harda murguda baki dan tasan koh ah mafarki ta auri Ahmad baza taji dadi ba, yana mugun son Sarah dan magana daya biyu sai ya kira sunan ta, kuma ita kanta Sarah tafi Teemerh hauka, ajiye friendship zatayi gefe ta ciwa Teemerh mutunci "Ae koh bai hanaki ba ni zan hanaki" taji muryan Asmah, saida zuciyanta yayi rawa kafin ta girgiza kai kadan, ina ita ina auren Najeeb yanada wannan, kuma ya fada mata yanasan matan sa, da wuya yaga laifinta in abu ya had'asu "Toh ke kuma awa?" Teemerh ta daure ta tambaya "Ni a matarsa" ta bata amsa confidently "Kuma baki isa aure mun miji akai sunan sa wajen boka ba. Mun fi karfin ki wlh" kuka Teemerh ta fara, Asma'u kuwa koh a jikinta ta wuce neman Najeeb, bata gansa bama Leemerh ta tambaya yanda ta shaida mata Najeeb ya fita hakan yasa ta bisa. Aameer kuma suna chan suna nasu, so yake ya fahimtar da ita amma taqi fahimta "Yanzu abunda kikayi wa Ilhaam ah idon duniya ya dace kenan?" ya tambaya rai bace "So kakeyi kace im wrong, right? Ae daman ba yau ka saba fada ba. Yaa Aameer you better stick to your head cewa Ilhaam bata sonka saboda haka ka daina rawan kafa akanta, if to say she loves you ae ta fito a gidan Yaa Anwaar in koh bata fito ba? Amma kaga tayi maganan ka aure ta?" Kallonta yayi kawae jin abunda tace kafin yace "Bakida magana daya wuce Ilhaam bataso na. That doesn't matter as long as I love her and I will do that till my last breath, yarinyan nan ta shiga matsala da yawa, kuma soyyayyah take bukata yanzu, saurin girgiza kai ta fara ta matsa baya "Then why do you marry me after knowing you are in love with someone else Aameer?" Ta fada tana kuka, kallonta kawae yayi baice komai ba ya dau key ya fita dan bayiso tana kuka. He love Ash damn much amma shi kansa ya rasa abunda yake damun sa.
*~*

💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now