💖💫RUDANI💖💫 71

71 25 73
                                    



Calm your mind and read confidentiality, Aameer is aliveness In Shaa Allah. Who will take the case after his death? Guys ponder! We need Aameer in this book as much as we need the lifesavers (Doctors).


Tashi tayi da sauri kaman ta tuna wani abu, kawae sai ganin journalists sun shigo tayi, share tambayoyin da suke mata tayi ta wuce CCU wajen da Aameer da Anwaar suke, Anwaar na rike da Defibrillator yana kan dannawa akan kirjin Aameer, he is doing that very fast yanda zuciyan zai amsa, tana tsaye tana kallo, ita bataji ma Aameer bayida rai ba haryanzu, she can feel that Aameer is alive, tana tsaye two of the cops suka dawo ganin en jarida sun dawo ya kamata su tsare wajen, tuni suka fara yada labaran Aameer ya rasu kaman yanda sukaji a bakin wata Nurse, Anwaar na ciki yana cigaba dayin abunda ya zama masa dole, machine inne ya fara kara kaman da sai kuma line in dake jiki ya fara motsi "Alhamdulillah" Anwaar ya fada a fili kafin ya ajiye defibrillator, yasan the hospital will be shut down saboda kuskuren da Yaa Hafeez yayi guda daya, Aameer's heart skipped a beat and he misunderstood it, he is an Orthopedic surgeon and Aameer needs a Cardiologist at that instant, thank God he arrived at time, he don't like attending to the media but he has to, hakan yasa ya fito, yana fitowa Ilhaam ta shige dan tabbatar wa da kanta, Xeenerh dake gefe ma ta shiga, da ikon Allah duk wanda suke wajen saida suka shiga, yana fita kuwa suka zagaye sa "Barrister Aameer's cause of death please, time and-" kafin ta karasa tambayan nata ya katse ta "Stop the propagation of the flawed news and dilate the literal one. Barrister Aameer is aliveness and under the care of some licensed Doctors" Alhamdulillah suka fara fada "Your name please" wata daga gefe ta amsa da Anwaar, kaman bazai fada ba yace "Anwaar Albaaz" ihu suka fara jin sunan, Anwaar in media kowa naso ya fara tura labaran "Aameer is alive and under the care of some certified Doctors as Dr. Anwaar Albaaz gives us self confidence. I am Usman bin Usman reporting from your favorite news channel. Aameer yana raye kuma yana karkashin kulawar wasu qwararrun likitoci kamar yadda Dr. Anwaar Albaaz yake bamu bayani. Ni Usman bin Usman ne ke rahoto daga tashar labarai da kuka fi so" ya sake Hausa version kafin akayi cutting, kusan a tare Shareef da Ashphert suka shigo dan yaji labaran koh ina, ita bata ma san abunda ya faru ba amma ganin mutane yasa ta razana, gashi kuma taga different tv stations, da gudu tayi CCU (Cardic Care Unit) dan ganin yanayin Aameer, she heaved a sigh ganin duk anata hamdala "Wae miye yake faruwa? Naga differents kind of people" ta tambaya bayan ta karasa wajen Aameer "That Yaa Hafeez is really unfit, gashi yanzu Ummi ma na kwance" Xeenerh ta fada "Toh wae saboda meyasa?" Ta sake tambaya, shiru duk suka mata tunda dai yanzu sun tabbatar da ransa ae shknn, Munnirah na gefe tana cigaba da share hawayen da kaman ba sharewa take ba, ita bata taba regretting rayuwanta irin na yau ba, akwae wanda koh ka musu laifi baka san yanda za'ayi ka fara neman gafara ba, and Aameer is one of them, taya zata fara cewan ta masa laifi? Ta dawo tace tayi wa Anwaar da Ilhaam laifi? Ihu tasa tareda sa hanu akai, da sauri Humainah ta matsa ta riketa "Calm down, he is alive" ta fada dan ta zaci kukan saboda Aameer takeyi, eh saboda shine amma different case, juyawa ah hankali Ilhaam tayi tana tafiyan kaman bazatayi ba Humainah ta jata "Ilhaam?" Ta kira sunan ganin she is so lost "For the safety of Barrister Aameer, we want you all out please" wata nurse ta shigo da policeman biye da ita "Yesmin" Xeenerh ta fada da gudu tayi waje tunawa da Yesmin da tayi, kwace hanunta itama Ilhaam tayi ta fita ta fara neman Ummi kafin duk suka fito, taje wajen Ummi kuma ta ganta amma kukan ma bai zo ba, ita kanta ma so take tayi kukan tasan the pain will be less amma ta kasa, fita kawae tayi dan tafiya gida, ita bazata sake dawowa bama, gani tayi Yaa Abu da Yaa Mahouz sun shigo, Aunty Nabeelah and some relatives daya kamata ace sunzo, koh gaisuwa batayi ba ta wuce Shareef da Yaa Farouq suna magana da wasu cops, ita kadai tana tafiya kaman baza tayi ba dan damuwan kanta yafi karfinta, ji tayi an jata gefe, tana kokarin kwace hanun ma Anwaar ya hanata, ganin yaki saketa ta tsaya ba tareda ta kallesa ba "Ilhaam" ya kira sunan yanda zataji amma koh kallon sa batayi ba, shi meyasa ma ya bari tazo, dafe kai yayi tunawa da ae baisan haka zai faru ba, kamata yayi ya juya ta to avoid any sickness forming in Ilhaam's head, she is trying to get into mental shock koh ba'a fada, she is not even thinking straight right now and he has to take care of that before it's too late "Allow your tears down. Please" kallon sa tayi kaman bata gane abunda yake fada kuma ta gane sarai, shi ta masa magana mana ma amma taki "Ilhaam" ya daka mata tsawa kawae attention ya dawo kansu, ganin haka ya jata suka fita, sai ganin Xeenerh, Aameen da Yesmin sukayi, sun samu tabar kuka after the assurance that Aameer is alive toh yanzu zataje gani wa idonta ne, ganin kaman hankalin Anwaar yayi gaba ta kwace hanunta da sauri ya sake rikota "Ilhaam stay still-" kafin ya karasa yaja hanunta da sauri suka matsa ganin motan Teemerh na shirin bigesu, da gudu ta fito tayi ciki ba tare da tsayawa wajen Anwaar ba dan ita wae a dole bata kula dasu bane kawae damuwan ta taji dagaske ne koh Aa, labari iri da kala ta fara ji wajen tun kafin masu abun su yanke shawara en jarida sun fara baza cewan za'a dakatar da Hafeez na shekaru biyu sannan Nigerian Medical Association (NMA) zasuyi honoring Anwaar kan cancanta da taimakon gaggawa, yanda wasu kece Aa Anwaar zai karbi hukuncin barin mara lafiya bayan yasan hakan zai faru, bata tsaya sauraron sauran shirmen ba ta wuce ganin Aameer, ganin mutanen sun kasa sun tsare hakan yasa ta koma baya, chan ta hango Munnirah ta karasa da gudu "Munnirah is he alright?" Kallon Teemerh tayi taja tsaki, tasan fa Teemerh ba damuwa tayi ba amma ji abunda takeyi kaman ta damu "Nasan baki damu koh yana raye koh Aa ba" ta bata amsa "Why will you say that? Aameer is one of the dear ones" harara mey ji da lafiya Munnirah ta bita dashi "Sai ki bari su Yaa Abu su fito sai ki shiga kiga Ummi" tace "Meya sameta?" Girgiza kai Munnirah tayi Teemerh kuma tayi ciki. Anwaar na wajen Ilhaam, ba maganan da bai fada ba amma taki kulasa balle koh kukan tayi, ya fada mata cewan Aameer is alive thousand of times amma bata amsa ba "Aameer is aliveness" ya maimaita kansa for the 1645th time "I know" ta bashi amsa for the first time bayan maganan da yatayi "Why are you doing all this?" Girgiza kai tayi "I don't know Anwaar, nima yanzu na tuna, I will go meet Aameer right now" ta fada amma bai saketa ba "Thank The Almighty ke kin dawo hankalin ki, don't try meeting him, you will end of hurting yourself again and again" kokarin fara kwace hanun tayi "You know his condition kuma ka barsa ka koma gida ae, leave my hand please" sai kuma ta fara kuka, tunda Anwaar yake this is the first time yayi farin ciki Ilhaam na kuka, yasan in batayi ba the thing will keep on eating her har taje ta sake samun wani matsalan kuma, yana jin ta fara kukan ya sake hanunta sai kuma ta tsaya kallon sa "Mugu kawae, dama so kakeyi na kuka" tana fada ta share hawayen ta koma ciki, shima binta yayi yaga Fatima kuma na fitowa tana ta faman share hawaye, the way she saw them crying breaks her heart, amma taga kaman sunki appreciating zuwan ta "Tunda kin lura da hakan sai ki koma gida kiyi zaman ki, zuwan ki bazai sa Aameer yaji sauki ba" ya bata amsa bayan ta gama masa narrating, ta samu tabar kuka amma Anwaar naso ta cigaba, shiru tayi gane shi fa Anwaar ka masa laifi daya ka shiga uku, he will try his best yanda bazaiyi fushi da mutum ba amma yayi shknn kuma, amma ae da sai ya duba how she came here out of love, she want not Aameer to suffer, so takeyi kawae Aameer yaji sauki, Aameer is suffering amma ita batada sa hanu cikin abunda ya faru da Aameer, da Ilhaam kadai takeyi "Ki wuce ki dauko Fadel ku koma gida, and with whose permission kika fito?" Shiru tayi dan ita dama tasan tunda wancan Yaa Ateeka'n nasu ta daina nuna tana santa dole haka ya faru, ita duk in tace musu abu shknn sai su wani dauka su zauna, toh ae sai su cigaba da zugasa sa "Anwaar nikam akwae mey zugaka ne? Nifa in kaga ka gaji da auren kawae ka sawwake mun nayi gidan mun-" kafin Teemerh ta rufe baki ya dauketa da mari to avoid the nonsense coming out of her mouth, banda rashin kunya yana ce ga abunda zatayi tana ce masa ba haka ba, kuka tasa da gudu ta fita kafin ma tayi dragging attention na mutane wajen, ita tarasa meyasa ma da ya fara fadan nasa batace toh koh ta bada haquri ba, duk tasan saboda Ilhaam yakeyi ae, dan ita ba daman Anwaar mata hukunci sai ta fara tunanin saboda Ilhaam yakeyi.

💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now