💖💫RUDANI💖💫 96

71 21 80
                                    


Aameer ke driving while Anwaar na danna waya har suka iso gidan su Teemerh yanda aka bude gate suka shiga, adan karkace Aameer yayi parking sannan suka fito sukayi main parlor, ba kowa a ciki hakan yasa suka zauna jiran Daddy dan yasan da zuwan su, basu jima suna zaune ba Daddy ya fito suka gaishe sa cikin girmama wa kafin suka fara abunda ya kawo su "Allah ya muku albarka, ban tab'a ganin laifin ka ba tun kafin koh bayan faruwan abun, bazan ce ka maidata koh kar ka maidata ba, zabi naka ne bamey maka dole" Daddy ya shaida masa "Tayi laifi, kuma ya mata hukunci. Tayi abunda ba daidai ba, amma ba laifi idan shi zai yafe mata" Aameer yasa baki "Hakane, Allah ya muku abarka ni zan wuce" yana fada suka tashi tare, saida ya fita kafin suka dawo suka zauna, wata maid ce ta shigo ta gaida su tare da ajiye musu abun sha "Fatima fa?" Aameer ya tambaya ganin bai ma ganta ba, he's sure batasan sun zo ba "Tana daki" ta amsa cike da ladabi "Call her please" ya umarceta "Okay" ta fada sannan tayi kitchen ta karasa kawo musu sauran abunda ya kamata sannan tayi sama domin kiran Teemerh, knocking tayi a nitse dan tasan halin Teemerh sarai wae dan ma da sauki ah haka "Come in" shiga tayi kanta a kasa ganin Teemerh kan abun sallah "Wai ana san magana dake" tashi tayi tana nade abun sallah tace "Wa?" Fuska ba yabo ba fallasa dai haka tayi maganan "Mijin ki" ta fada calmly gudun kar tace ex-husband su b'ata da Teemerh dan yanzu sun fara shiri, Teemerh is a better version "You mean Anwaar?" Ta tambaya cikeda mamaki hakan yasa Fadel kallonta "Eh shi" ta amsa a nitse "Kice ina zuwa then, ga Fadel ki fara kai masa shi" da toh ta amsa sannan ta dauki Fadel dake faman sallah shima suka fita, Fadel sai murna yakeyi dan ya gane Baban sane yazo, bayi wani spending quality time da Anwaar dan yafi zama gidansu Teemerh. Veil nata kawae ta dauka ta bulbula perfume ta fice, saukowa takeyi ah hankali har ta karasa saukowa kanta ah kasa dan mugun tsoron Anwaar take, ta iya rashin kunya harda Yaa Xee amma Anwaar dai tayi concluding sonshi take shiyasa take rage masa "Ina yini?" Ta gaishe su suka amsa in unison "An yini lafiya?" Anwaar ya tambaya yana rike da Fadel "Lafiya alau" Fadel ya amsa cikin magana na yara "No bada kai akeyi ba" Aameer ya fada hakan yasa Fadel barin wajen Anwaar zuwa wajen sa "Hassana" ta kira maid nasu hakan yasa tazo da sauri "Dauki Fadel anan" ta bata umarni nan ta dauki Fadel suka tafi ita kuma Teemerh ta nemi waje ta zauna "Daman abunda ya kawo mu shine-" kafin Aameer ya karasa ta tsaidashi "I knew very well what brought you guys here, but before any of that forgive me Aameer, I misuse you-" kafin ta karasa ya tsaidata "Teemerh please no" yayi saurin tsaidata "Let bygones be bygones tunda ita Ilhaam ta yafe ae shikenan. I would never find it hard to forgive you, na dade da yafe miki, just try regaining your respect in my eyes" shiru tayi ta gama jin sa "Thank you" ta fada ah hankali bayan ya karasa "Sai ka fito" Aameer na fada ya tashi domin fita saboda ya basu waje, shiru wajen yayi ba wanda yayi magana, sun kai 5mins kafin ah hankali Teemerh tace "How's Ilhaam and your little star?" Murmushi yayi jin abunda ta fara tambaya, and the way she put Afraah's name in the sentence sits right "They are fine, Ilhaam is the reason am here" kallonsa tayi dan dama tasani, dan kansa kam ba zuwa zaiyi ba "Bansan ta ina zan fara bada haquri ba, amma inaso ka yafe mun duk abunda nayi" shiru yayi jin ta fara bayani, Fatima tanada haske sosai amma ta danyi duhu kuma ta rame "Kinyi sallah?" Ya jeho mata tambaya, yes tayi missing yanda yake tambayan ta Sallah sai gashi ta sake ji after a long time, bayan basu tare kuma, taso da suna tare yaga how she changes, gyad'a masa kai tayi ah hankali ganin yana kallonta "Marriage can be a test from Allah, no matter how good a person is, yet our character plays a pivotal role in it, and we can't blame destiny for our behavior. If you really believed in Allah and the last day then you shouldn't have done what you did, our destinies were written before our birth Fatima, and you were part of mine, our marriage, and everything that had happened was written. Ita fa Ilhaam da kike kishi da duk haukan da kikeyi kanta ban tab'a santa ba itama sai lokaci guda, nasan kinsan na tab'a san Yesmin amma ba Ilhaam ba, Ilhaam was just effective and had some impact on me, lokaci guda kawae na fara santa" ya fada ah dame dan kuskuren farko daya fara shine sawa ransa bazai so Ilhaam ba, he hates to remember abokansa na son matan sa, it was a test from Allah saboda Ilhaam is not a vulgar balle ace abunda ke attracting nasu kenan, gosh we learned from our mistakes, kallon sa Teemerh tayi hawayen idonta ya fara gangaro wa "Nayi kuskure sosai, kuma inda na fahimci komai da wuri da duk haka bai faru ba, I saw that epistle before Ilhaam that day, naga duk abunda Xeenerh ta rubuta and how Ilhaam was a game to you. Na kasa yarda koh da na karanta, ah lokacin nasan nayi kuskure, inda na zauna lafiya da kowa da ah hankali zan zama nice wanda zaka fara ma irin san da kake yiwa Ilhaam, ba santa kakeyi ba, tausayin ta kawae kakeyi. Ka auri Ilhaam after she lost her pride, you don't want her to question her worth, she was traumatized kaman yanda kullum kake fada, shiyasa ka yanke shawaran zama abokinta yanda zata yarda dakai har ka fara kula da ita, kake biye ma duk abunda tayi saboda ta samu lafiya and make her fall for you again. Kana cikin kula da Ilhaam ni kuma ka aureni, am not having your time saboda kana kulawa da Ilhaam. Kaqi bani mahimmanci saboda kar tayi zaton zaka fara mata walaqanci saboda kayi aure ita kuma she was a trash that has no pride. Anwaar nayi kuskure nima, saboda nayi zaton idan Ilhaam ta rasa pride nata bazaka aureta ba, but you proved me wrong, ka gwada mun Ilhaam kakeso ba jikinta ba. I was wrong, wrong, and I lost it" ta maimaita wrong har sau biyu sai kuma ta cigaba da kuka "I love you, yes I love you, Fatima. What you have always wanted huh? But you know what? My heart believes you so much that I don't believe any of your deeds. I realized sanki nakeyi shiyasa bani ganin laifin naki" kallonsa tayi hawayen idonta na cigaba da sauka as he chuckled in pain "Ilhaam tana sanki Fatima, tun kafin muyi aure batada magana sai naki. Amma ke? Tambaya daya zan miki, meyasa baki santa haka?" Ya tambaya sai kuma ya girgiza kai sanin tambayan baida amfani "Saboda kana santa" ta bashi amsan dagaske hakan yasa ya kalleta "Gani nake idan kana santa bazan samu soyyayyan kaba, gani nake soyayyan tane ya hana ka soni. Kuma ae itama bayan ka aureni nunawa tayi bataso kuma ranta ya baci. Nunawa take tanada iko akan ka" ta fada kanta tsaye danta rantse bazata sake masa karya ba "Batada iko akaina? Fatima accept that you married Ilhaam's husband please. She came first, and you were a second wife for a reason, first come first serve. So you married Ilhaam's husband" shiru tayi jin haka, ae tasan da haka kuma bawae ta karyata bane amma the things are much "Yanzu miye matsayin aurena dakai?" Ta tambaya ah hankali "Ki kawo mun Fadel" ya fada ba tareda amsa tambayan taba, tasa ah ranta this will be the last time da zata tambayi Anwaar akan auren su kawae, batace komai ba ta tashi tana cigaba da share hawayen ta kawo masa Fadel kaman yanda ya bukata ita kuma ta wuce wajen Yaa Sakina dan mata kuka, Yaa Sakina qanwar Daddy ne kuma ita ke kula da kusan komai na gidan yanzu, Teemerh found a mother in Yaa Sakina dan haka kawae ma tana sata suyi sallah su roki yafiyar Allah. Teemerh najin maganan Yaa Sakina sosai dan dama Mummy che take hana su muamala da dangin Daddy "Kina tunanin za'ayi wa mutum kishiya sai ya zauna yana farin ciki?" Ta sake jefo mata tambaya bayan ta gama fada mata yanda sukayi da Anwaar hakan yasa Teemerh d'agowa jikinta "Not all second wives come in intending to displace but many do Fatima, even you went into that marriage to displace Ilhaam and make her a trash" kallonta Teemerh tayi jin haka "Eh, kin auri Anwaar kuma kinaso kiyi replacing Ilhaam sannan ki fitar da ita" ta maimaita mata "Aurenki akayi kaman yanda aka aureta, tunani zata fara anya santa yakeyi ya aureta kuwa? Aurenta da wata guda aka sake naki. And polygamy most times is not sweet, so the wife coming in will be blamed as the source of this disruption, and the anger will be directed at you the second wife. And why would any sane second wife think that first wife will not be upset? This feeling is normal Fatima, there is no way any woman would enjoy sharing her husband, ki yarda you're a source of pain to Ilhaam" gyada kai ta fara after putting herself in Ilhaam's shoe, ba yanda za'ayi tabar wanda ya mata wannan abun ya zauna lafiya, but compared to Ilhaam ta daure "Allah ya miki albarka, yanzu ya maganan auren naku?" Sunkuya wa tayi kawae cikin rasa abun fada hawaye ya cigaba da aikinsa "Go to him, idan ba aure tsakanin ku akwae yaro tsakanin ku, try maintaining the bond" share hawayen tayi ta tashi ta fita kaman yanda Yaa Sakina tace, tana fita Yaa Sakina ma tabi bayanta "Ina yini" ya gaisheta ganin yanda taja Fatima jikinta "Lafiya qlau Anwaar, ya kowa ah gidan?" Yace "Suna lafiya Yaya" ya amsa ah nitse "Kayi hakuri da duk abunda ya faru sannan ka yafe mata" ta fada sannan ta karbi Fadel suka bar wajen, by this time kukan Teemerh ya tsananta kuma tana nadaman duk irin abunda tayi da wanda su Aunty Sham suka sa tayi "Fatima, na yafe miki. Tunda Ilhaam ta yafe nima zan iya yafewa kuma na fada miki tun ah farko na yafe miki, amma yafiyan Allah ya kamata ki nema ba nawa ba" ya maimaita mata "Ina neman yafiyan Allah, yafiyan ka kadai ya rage dan duk na tambaye su yafiya suma" ta bashi amsa "Nima na miki laifi, forgive me too" saurin girgiza kai tayi dan wlh Anwaar bai mata komai ba, yana adalci tsakaninta da Ilhaam, in tace baya yi ta masa karya, san Ilhaam bai rufe masa ido ba "I knew Ilhaam sacrificed many things to be with me and her happiness is one of them. But you sacrificed some things too. You gave birth to Fadel, kuma kin zauna dani bayan kinsan bani sanki lokacin" saurin kallonsa tayi "Meyasa toh bakaso na bayan kasan hakan?" Yace "You are so beautiful, you are good in your own ways amma kin kasa fahimtan love can never be force, kinada kyau and everything bashi zaisa naso ki dole banyi niyya ba" tayi shiru ma ta kasa magana, gaskiya Anwaar ya fada, tanada kyau kuma ae Ilhaam tanada, kenan in kyau yake bi ya samu, in hankali yakeso ma ya samu, all this aside komai yakeso ma zai samu wajen Ilhaam, ah hankali tace "Amma yanzu kana sona?" Murmushi yayi kawae jin tambayan nata "I loved you kafin wannan abubuwan su faru. Amma yanzu bansani ba. You caused everything and made me and my family fall for it. Sorry" ya fada ah karshe "Nice wanda zan bada haquri. Ya Afraah?" Ta tambaya dan chanja wancan zancen da kuma chanja masa mood and luckily yayi murmushi "She's good, tana kuka kaman Ilhaam" murmushin tayi itama ganin yana farin ciki, abunda ya kamata ya faru kenan fa tunda, amma tasa Anwaar ya sota dole kuma hakan bai dace ba, Anwaar is attached to her and attachment is a poison, yeah shakuwa yafi soyyayyah zafi, ta cuci Anwaar sosai tunda tasa ya sota dole, love was not meant to be force but she forced him, wannan cutarwa ne "Ka soni ne saboda ba yanda ka iya, I and my relationship was forced on you kuma duk bai kamata ba. Na fahimci cewa ba'a tilastawa so Anwaar, kuma-" saurin tsaidata yayi "Fadel fa? Zan iya sake ganin sa?" Ta mugun gane Anwaar is avoiding everything kanta yanzu, amma ba laifin sa bane "Yaushe zaka daukesa? And I wanted to ask wani school za'a saka shi?" Ta tambaya "Yanzu Ilhaam batada lafiya, koh lil Ash ba wajenta take ba. Amma by this time nasan zasu maida mata yarinyan ta dan jikin da sauki" ya mata bayani ah takaice, bayan ta bashi amsa ta tashi dan dauko masa Fadel. Ah wajen sa Fadel yayi bacci kafin ya fita ya samu Aameer dansu tafi. Aameer ya sauke Anwaar gida lafiya shi kuma ya wuce "Angelic ya jikin? Koh wani abun ne?" Ya tambaya dan tabbatarwa "Ash ta hanani bacci sai kuka ba dole ka tambaya ba" samun waje yayi ya zauna ya fara dariya danshi ya zaci wani abun akayi ma Ilhaam "Allah kayita mun dariya sai na koma wajen Ummi nabar maka yarinyan ka" ta fada kaman zatayi kuka "No you don't have to do this, now ke ki kwanta kiyi bacci and I will look after her" ya fada sannan ya karasa wajen, kallon sa tayi dan bataji mey yace ba saida ta maimaita "Very Own, are you sure?" Gyad'a kai yayi "Yea" yana fada ya dauki Afraah, dama yayi zaton zai dawo ya samu an kawo ta and luckily "How sweet, I love you so much Very Own" ta fada da wide smile "I love you more" ya fada sannan ya fita da Afraah dan su barta tayi bacci, ita da aka bari tayi bacci kuma ta sake binsu bayan 'Thank you' messages na Teemerh sun shigo mata "Angelic am I save? Kika ce bacci zakiyi" shiru tayi kuma ta rasa ta ina zata fara, tanason ta tabbatar dagaske yaje wajen Teemerh kaman yanda tace koh Aa, daya side in zuciyanta kuma tsoro take "Bakomai, I want to be looking at you two" baice komai ba dan ba yau yasan Ilhaam ba, yasan da abunda take boyewa, ganin tayi shiru shima bai ce komai ba harta fara bacci wajen. Saida ya tabbatar Daisy tayi bacci, kafin ya dawo ya dauki Ilhaam zai kaita daki, yana daukanta ta farka "Saukeni" ta fara kokarin sauka "Yi shiru koh na yarda ke" shiru tayi though tasan ba yarda itan zaiyi ba har suka karasa dakin ya ajiyeta kan accent chair shi kuma ya zauna daga ta k'asa "It's two options, you either sleep peacefully or tell me what's bothering you" shiru tayi ta sauke ido kasa hawaye ya taru idon "Teemerh called and thank me dazu, yanzu kuma ta turo message wae tace kaje wajenta" sai kuma hawayen ya sauko, qin dagowa tayi gudun karya gani, ah hankali ya dago fuskanta and he met the biggest surprise, Ilhaam na kuka, tun bayan auren su fa batayi kukan nan ba sai da bata da lafiya, sai yau saboda wannan "Are you sure you are ready for this? Kefa kikayi insisting naje, I don't want you crying" shi daman yasan yanda take kishi da Fatima lokaci guda tace ta bari ae bai yiyuwa "I am ready Very Own. Amma dole naji tsoro" patting bayanta ya fara ah hankali, shifa haryanzu baice zai dawo da Teemerh ba, amma tunda Ilhaam tace zai dawo da ita saidai ba yanzu ba, kuma shi kansa baisan lokacin ba. Yana fatan kafin lokacin Ilhaam ta chanja ra'ayi "Meyasa kike san hakan?" Ya tambaya ah dame "She loves you, she did everything out of love, ba abunda soyyayyah bayi sawa. Nayi adalci wa kaina idan na rabata dakai? Tasha wahala itama, koh san wanda bayi sanka aka barka dashi kadai ya isa, kuma laifin tane? I don't want to say but her Mum is to be blamed for everything tunda abunda ta koya mata kenan. Wani lokacin laifin iyaye ke shafan yara, even our Ummi and Mami were wrong, we grew separately with our parents due to some reasons, ya dace muyi rayuwa wani wajen daban suma suna wani waje in the name of yanda muke akwae securities?" Kallonta yayi jin how her words are making sense "Inda ina wajen manya, someone like Yaa Abu da duk abunda tasa Yaa Aameer yayi da bai faru ba tunda ba yanda za'ayi ya shiga yanda yakeso gidan Yaa Abu, to talk more of going to my bedroom. Being one of the Albaaz doesn't guarantee happiness, but we will be happy nah?" Tana fada hawayen da take boyewa ya sauko, saurin sharewa tayi tana murmushi dan ba niyyanta kuka ba "We'll be happy In Shaa Allah" ya maimaita tareda rike hanunta suna murmushi, but it's a painful one, sure duk abunda Ilhaam ta fada gaskiya ne "I would like to love you till eternity" ya fada tareda tashi a kasan ya zauna a kujeran ya sata a cinyansa giving her a peck ah forehead nata "Zaki iya zuwan Chad? The kingdom want seeing the 'She' that stole my heart" murmushi tayi bata amsa ba, amma yanda ya manna ta da jikin sa he can hear it "Sun sanni fa, we went there the other times" ta bashi amsa "Ban aure ki ba lokacin, yanzu kuma you are mine" shiru tayi kawae tana murmushi, ita mantawa take da he's somehow, no someone from the kingdom, dole yana acting as one sometimes "Yaa Anwaar" ta fada ah hankali hakan yasa ya kalleta "Would you choose me again?" Ta tambaya bayan ya kalleta "If life is repeated a thousand times. It's still you, you, and again, you Ilhaam" ya bata amsa "Alhamdulillah" ta fada ah hankali amma yaji, itafa bata tab'a tunanin Anwaar zai sota haka ba, amma see who is loving her tremendously "You are mine, mine alone Ayatullah" wow just a wow, tsayawa kallonsa tayi blinking her eyes, how the name sound sweet ah bakin Anwaar, yes his first time calling her Aya, bai tab'a fada ba sai yau, ashe duk abunda akeyi yana kula, yana jin Ummi na ce mata Aya amma bai tab'a trying ba "I love you, but I need to sleep right now. Good night love" tana fada ta fara addu'an baccin, murmushi yayi ganin haka "Let's pray before sleeping" yayi suggesting "Toh barin yi alwala" ta fada da murmushi ta sauka jikinsa.


💖💫RUDANI💖💫Where stories live. Discover now